Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RA'AYINMU

Har Yanzu Kan Buƙatar Muhimmanta Waziran Makarantu

by Tayo Adelaja
October 10, 2017
in RA'AYINMU
3 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

A makon jiya mun fara bayani a kan muhimmancin aikin waziran makarantu a ɗaukacin makarantun da muke da su a ƙasar nan musamman makarantun gwamnati waɗanda ba su cika mayar da hankali a kai ba saɓanin masu zaman kansu.

Ƙasashen duniya da suka cigaba, sun lura da muhimmancin waɗannan wazirai, shi ya sa ba su yin sako-sako da su a makarantunsu. A ƙasar Japan, waziran makarantu suna taimaka wa ɗalibi ya fahimci kansa (wurin da yake da ƙarfi da ɓangren da yake da rauni), ya zama mai ra’ayin kansa, ya iya tsara rayuwarsa da irin matakan da zai bi ya gyara tarnaƙin da ka iya masa barazana ga cimma burinsa. A Faransa kuwa, wacce ta fara amfani da waziran a makarantun sakandare a 1922 sannan ta yi cikakken shigar da su cikin tsarin iliminta a 1930, ta wajabta yin aiki da waziri a kowace makaranta. Ita kuwa ƙasar Tailan, malaman da ke koyarwa a makarantu akan horas da su aikin wazirci a makaranta. Ƙasar Honkon, ta tabbatar da aikin wazirin makaranta a ɗaukacin cibiyoyinta na ilimi. Sauran ƙasashe irin su Andulus (Spain), Fotugal, Danmak, Beljiyom, Italiya, Jamhuriyar Silobakiya da Nowai sauran su, sun samar da shafuka na musamman a intanet da al’ummar ƙasarsu ke amfana da waziran. Amma mu a Nijeriya, ina aka bar mu?

samndaads

Waziran makarantu suna taimaka wa ɗalibai su zama masu ƙwazo. Masana ne akan basira da kaifin ƙwaƙwalwar kowane ɗalibi. Sun fahimci yanayin muhallin karatun da ya fi dacewa da kowane ɗalibi. Waziran makarantu suna yauƙaƙa zumunci da fahimtar juna a tsakanin malamai da iyayen yara, kana sukan daidaita tunanin ɗalibi ya fuskanci burin da ya tasa a gaba.

Galibin matsalolin da suke hana mu sakat a ƙasar nan a wannan zamanin za a iya magance su tun a matakin makarantun sakandare. Saboda a nan ake cusa wa yara irin ɗabi’un da ake son gani a tare da su idan girmansu ya kai isa-matuƙa. Babbar hanyar hakan kuwa ita ce ita ce tabbatar da samar da waziran makarantu a dukkan makarantun sakandare. A matsayinsa na ƙwararre, wazirin makaranta  yana da ƙwarewar da zai hana ɗalibai mu’amala da ɓata-garin abokai cikin ruwan sanyi, ya hana tserewar yara daga makaranta, ya daƙile yawaitar ɗaukan juna biyu a tsakanin ‘yanmata masu tashen balaga a makarantu, ya raba matasa da ɗabi’ar shaye-shaye wadda ta zama ruwan dare a manyan makarantunmu da ƙanana. Bugu da ƙari, duk jami’in da aka horas a fannin kuma ya horu horuwa, yana da ƙwarewa wurin rigakafin tayar da zaune-tsaye a makarantu, da kawar da ƙyamar juna a tsakanin jama’a da kuma tabbatar da zaman lumana da aminci duk da bambancin ƙabila da addini. Har ila yau, ya san hanyoyin rigakafin hana mugun hali samun mazauni a cikin zukata, wannan yana da matuƙar tasiri a wurin ɗaliban da rayuwarsu ta gaba, kasancewar ‘kara tun yana ɗanye ake tausa shi; idan ya bushe sai dai ya karye!

Idan an muhimmanta aikin waziran makarantu tare da shigarsu cikin tsarin ilimi na gwamnati, za a samu sauƙin ɓarayin gwamnati da magoya bayan masu wargaza ƙasa ta hanyar ta’addanci ko tawaye, kasancewar hatta yaran da suke fita daga makarantu ba tare da sun kammala ba, jami’an suna da ƙwarewar da za su ɗora su a turba mai kyau na koyon sana’o’in da suka dace da su.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnan Jihar Sakkwato, Aminu Tambuwal yayin da yake amsa tambayoyin ‘yan jarida bayan ganawar da suka yi da Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, jiya a fadarsa da ke Abuja (Hoto: NAN)

Next Post

Yaƙi Da Cin Hanci: Dalilan Da Suka Sa EFCC Da ICPC Suke Samun Naƙasu –Akin Olumiji

RelatedPosts

Kannywood

Alhakin Shiga Tsakanin ’Yan Kannywood Da Afaka Ya Rataya A Wuyan Ganduje

by Muhammad
5 days ago
0

Masana sha’anin shari'a suna cewa, da a yi kuskuren hukunta...

Dambarwar Najeriya Cikin Shekaru 60: Murna Ya Kamata Mu Yi Ko Kuka?

Yayin Da Nijeriya Ta Cika Shekaru 60 Da ‘Yancin Kai…

by Muhammad
5 months ago
0

A jiya ne Nijeriya ta yi bikin cika shekaru 60...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Kafa Cibiyar Jinkan Tsofaffi – Minista Sadiya

Kafa Hukumar Kula Da Nakassasun Nijeriya Da Dawo Da Martabarsu

by Muhammad
5 months ago
0

A ranar Litinin, 24 ga Agusta na 2020 ne, Shugaban...

Next Post

Yaƙi Da Cin Hanci: Dalilan Da Suka Sa EFCC Da ICPC Suke Samun Naƙasu –Akin Olumiji

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version