Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Hassan Hassan Ya Shawarci Iyalan Marigayi Maula Idris Da Su Rike Juna Da Amana

by
4 years ago
in LABARAI
1 min read
Hassan Hassan Ya Shawarci Iyalan Marigayi Maula Idris Da Su Rike Juna Da Amana
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

A shekaran jiya ne Allah ya yi wa daya daga cikin ‘yan jaridan da suka yi hidima wa jihar Bauchi, Alhaji Maula Idris wanda ya kammala aikinsa a matsayin babban Daraktan da ke kula da gidajen rediyon al’umma da suke jihar Bauchi (BRC) rasuwa, ya rasu ne a sakamakon rashin lafiyar da ya yi fama da ita.

An yi masa jana’iza da  kaisa makwancinsa a jiya Juma’a, inda ‘yan jarida da dama suka nuna kaduwarsu da rashin nasa, kana suna bayyanasa a matsayin mutumin arziki.

A lokacin da wakilinmu ya raka tawagar babban malami a kwalejin kimiyya da fasaha mallakin gwamnatin tarayya da ke Bauchi, Hassan Alhaji Hassan kai gaisuwar jaje da ta’aziyya ga iyalan mamacin a gidan marigayin da ke Dutsen Tanshi, babban malamin ya shawarci iyalan marigayin da su rungumi juna da amana.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Sauyin Sheka Yasa Majalisar Dokokin Kano Ta Dage Zamanta Na Ranar Litinin

Deborah: Kungiyar Gwamnonin Arewa Ta Bukaci A Zauna Lafiya

Ya ce, “Girma ya zo muku, tabbas dukkaninku girma ya zo muku. Wannan hanyar haka take, kowa wa’adinsa yake jira, Allah ya gafarta wa mahaifinku ya sanya aljanna ta kasance masa gida.

Ya shaida wa babban dan marigayin da kaninsa cewa, “ina shawartarku ku kasance masu kula da junaku, dukkanin wani da zai nemi raba kanku kada ku yarda, ku tabbatar da rungumar kannenku da amana ku, kuma jure nauyin girma da Allah ya daura muku,” Inji Hassan Hassa

Kana ya kuma shawarcesu da su ci gaba da runguma ababe masu kyau da mahaifinsu ya rasu ya barsu a kai, ya kuma karfafi ‘ya’yan marigayin dangane da kula da sha’anin iliminsu domin inganta rayuwarsu.

Babban malamin ya yi addu’a ta musamman ga marigayin, yana bayyanasa a matsayin mutumin arziki wanda ya jajirce wajen yin aiki tukuru.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Bankin Duniya Ya Ya Ba Jihar Kaduna Lambar Yabo

Next Post

Kwamitin Bincike Ya Gayyaci Editan Daily Nigerian

Labarai Masu Nasaba

Zargin Sauyin Sheka Yasa Majalisar Dokokin Kano Ta Dage Zamanta Na Ranar Litinin

Zargin Sauyin Sheka Yasa Majalisar Dokokin Kano Ta Dage Zamanta Na Ranar Litinin

by
13 hours ago
0

...

Deborah: Kungiyar Gwamnonin Arewa Ta Bukaci A Zauna Lafiya

Deborah: Kungiyar Gwamnonin Arewa Ta Bukaci A Zauna Lafiya

by
16 hours ago
0

...

Ganduje Ya Umurci Bala Ya Kula Da Ofishin Shugaban Ma’aikata Fadar Gwamnatin Kano

Ganduje Ya Umurci Bala Ya Kula Da Ofishin Shugaban Ma’aikata Fadar Gwamnatin Kano

by
20 hours ago
0

...

Deborah: Matasan Musulmai Ba Su Kona Min Gidana Ba —Bishop Kukah

Deborah: Matasan Musulmai Ba Su Kona Min Gidana Ba —Bishop Kukah

by Abubakar Abba
23 hours ago
0

...

Next Post
2019: Miliyoyin Nakasassun Kano Sun Gindaya Wa Ganduje Sharadi – Abba Sarki

Kwamitin Bincike Ya Gayyaci Editan Daily Nigerian

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: