Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Hukumar EFCC A Kaduna Ta Gurfanar Da Wani Matashi Bisa Zargin Damfara

by Tayo Adelaja
September 14, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abubakar Abba, Kaduna

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa da yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa wato EFCC shiyyar jihar Kaduna ta gurfanar da   wani mai suna Paul Ehiemau da take zargin kwararren ne wajen damfara.

samndaads

Paul, an gurfanar dashi ne a gaban Alkali  Darius Khobo na Babbar kotun jihar ranar Talata,  bisa zargin damfara ta naira miliyan goma sha biyar.

Hukumar ta gurfanar da Paul ne tare da kamfaninsa mai suna Blackrock Trading Logistics da ake zargin da shi ne yake gudanar da damfarar.

Ya yi karyar cewar, shine yake wakiltar kamfanin na STOJ Oil da Gas cewar kamfanin ne, ya ba shi damar gudanar da cinikayya.

Wadanda ake zargin su biyu, sun amsa laifin nasu. Lauyan Hukumar Sa’ad Hannafi Sa’ad ya roki kotun da ta sanya don yanke wa wadanda ake tuhuma hukunci, da kuma tura su gidan kaso ajiya.

Mai kare wadanda ake zargin M.A Shariff ana nashi jawabin, ya yi duk iya kokarinsa don neman a bada belin ta hanyar fadi da baki wadanda ake zargin amma Alkalin kotun yaki amincewa da hakan, inda ya umarci lauyan da ya rubuta a rubuce.

Lauyan ya nemi belin ne, a ka uzurin cewar wanda ake zargin na farko Paul, bai da lafiya, inda ya roki kotun da ta ajiye shi a kurku har zuwa ranar da za a saurari bukatar belin nasa. Alkali Khobo ya bukaci lauyan da gabatar wa da kotun shedar takardar cewar Paul bai da lafiya, inda kuma lauyan ya kasa gabatar da takardar.

Alkalin ya yanke hukuncin da a kai Paul ajiya a gidan yari har zuwa ranar sha tara ga watan Satumbar shekarar don sauraron takardar bada belin.

SendShareTweetShare
Previous Post

Masu Hannu Da Shuni Su Taimaka wa Mabukata —Hajiya Maimuna

Next Post

Rikicin APC Akida Da El-Rufa’i: Ko Zai Haifar Wa APC Da Mai Ido A Kaduna?

RelatedPosts

Gina Hanyar Ruwa: Babu Kudin Kowa A Cikin Wannan Babban Aiki, Inji Mai Turaka

Gina Hanyar Ruwa: Babu Kudin Kowa A Cikin Wannan Babban Aiki, Inji Mai Turaka

by Daurawa Daurawa
5 hours ago
0

Mai taimakawa gwamna Masari akan wayar da kan jama’a akan...

’Yan Sandan Kano Sun Cafke Mace Mai Garkuwa Da Mutane

’Yan Sandan Kano Sun Cafke Mace Mai Garkuwa Da Mutane

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kano ta shaida cewar wata mace...

Ta’aziyar Rasuwar Sam Nda Isaiah

Sam Nda-Isaiah Ya Rasu Lokacin Da Ake Tsananin Bukatar Gudunmawarsa – Jami’ar Jos

by Sulaiman Ibrahim
4 days ago
0

Shugabannin jami’ar Jos sun bayyana rashin jin dadinsu dangane da...

Next Post

Rikicin APC Akida Da El-Rufa’i: Ko Zai Haifar Wa APC Da Mai Ido A Kaduna?

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version