Khalid Idris Doya">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Hukumar Farfado Da Shiyyar Arewa Maso Gabas Ta Tallafa Wa Gombe Da Kayan More Rayuwa Ta Hannun Gidauniyar Jewel

by Khalid Idris Doya
February 13, 2021
in LABARAI
2 min read
Hukumar Farfado Da Shiyyar Arewa Maso Gabas Ta Tallafa Wa Gombe Da Kayan More Rayuwa Ta Hannun Gidauniyar Jewel
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Hukumar farfado da shiyyar Arewa Maso Gabas ta bada kyautar kayayyakin abinci da kuma wasu nau’in ababen more rayuwa domin tallafa wa mabukata na miliyoyin naira ta hannun gidauniyar Jewel Care Foundation domin rabawa ga masu bukatar hakan.

Uwargidan gwamnan jihar Gombe, Asma’u Muhammadu Inuwa Yahaya ca ta amshi kayan tallafi da zimmar tsara yadda za a raba ga wadanda suka dace domin inganta rayuwar talaka ta karkashin gidauniyar nata na Jewel da aka samar domin tallafa wa rayuwar mabukata musamman mata da matasa.
Bayanin hakan na kunshe ne ta cikin wani sanarwar da Bintu Aliyu Sunmonu, Jami’ar watsa labarai ta ofishin matar gwamnan jihar ta fitar, inda ta nuna cewa mabukatar da suke halin neman tallafin rayuwa ne za su ci gajiyar kayan abinci da na more rayuwar.
Da take karbar tallafin, uwargidan gwamnan Hajiya Asma’u ta yaba wa shugaban kasa Muhammadu Buhari dangane da shirin gwamnatin tarayya na agaji, wanda ta ce ya zo daidai da shirin ta na tallafawa masu fuskantar barazanar rayuwa tare da yaki da cin zarafin mata da rashin daidaiton jinsi a cikin al’umma.
Ta kara cewa, “kungiya ta mai zaman kanta tana kulawa da mabukata tare da samarwa mata da matasa abun dogaro da kai domin sa’ayin ganin rayuwa ta inganta domin samun ci gaba mai daurewa.”
Hajiya Asma’u Yahaya ta kuma yaba wa kokarin hukumar da ta kawo kayan inda ta tabbatar da adalci wajen rabon kayan ga mutanen da suka dace ba tare da nuna son kai ko fifiko ba.
Kamar yadda sanarwar ke cewa, kungiyar matar gwamnan jihar ta Jewel ta dauki tsawon lokaci tana gudanar da ayyukan jin kai da kuma bada tallafi ga rukunin jama’a musamman mata da matasa, sai ta nuna cewa za ta ci gaba da aiwatar da irin wadannan ayyukan domin kyautata rayuwar al’umman jihar Gwambe.
Da ya ke mika kayan ga uwargidan gwamnan jihar Gombe, shugaban hukumar farfado da shiyyar arewa maso gabas, Muhammad Goni Alkali, ya ce, sun kawo tallafin ne don a rage radadin illar annobar cutar Korona a jihar.
Shugaban ya kara da cewar ban da tallafin, sun zo jihar nan don su tattauna da gwamnatin jihar tare da kaddamar da wasu ayyuka dukka domin kyautata rayuwar jama’a.
Shugaban ya taho tare da shugaban kwamitin majalisar dattawa akan hukamar farfado da shiyyar arewa maso gabas da babban Daraktan ayyuka da na jin kai na hukumar, kamar yadda sanarwar ke cewa.
Kayayyakin da aka bayar sun hada da kayan  gini, buhunan shinkafa, tabarmai, katifu, taliya  dandano, man girki da sauran su.

SendShareTweetShare
Previous Post

TETFUND Ta Yi Kokari A Ci Gaban Ilimin Yobe Amma Muna Son Kari- Gwamna Buni

Next Post

Za iya Amfani Da NIN Don Gano Bata-Garin In ji Ganduje

RelatedPosts

Jami’ar Tarayya Ta Gusau Ta Musanta Labarin Harin ‘Yan Bindiga

Jami’ar Tarayya Ta Gusau Ta Musanta Labarin Harin ‘Yan Bindiga

by Khalid Idris Doya
9 hours ago
0

Daga Hussaini Yero, Shugabannin Jami'ar gwamnatin Tarayya dake Gusau (FUG)...

An Yi Wa Buhari Da Osinbajo Allurar Rigakafin Korona

An Yi Wa Buhari Da Osinbajo Allurar Rigakafin Korona

by Khalid Idris Doya
14 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim An yi wa Shugaba Muhammadu Buhari da...

Mukabalar

Kotu Ta Dakatar Da Yin Mukabalar Sheikh Abduljabbar Da Malaman Kano.

by Khalid Idris Doya
19 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Wata kotu a Jihar Kano ta...

Next Post
Kananan Hukumomin Jihar Kano

Za iya Amfani Da NIN Don Gano Bata-Garin In ji Ganduje

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version