Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

Hukumar Kwastom Ta Gurfana Gaban Kotu Kan Kisan Matashi A Kebbi

by Muhammad
March 9, 2021
in LABARAI
2 min read
Kwastom
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Umar Faruk,

Hukumar Kwaston ta Nijeriya ta gurfana a gaban Babbar Kotun Tarayya dake zamanta a Birnin-Kebbi karkashin Mai Shari’a Sunday Bassey Onu a jiya bisa sauraron karar da mahaifin Marigayi Abdulrahman Sani Bunza ya shigar kan zargin daya daga cikin jami’an hukumar ta Kwastom da harbe masa damsa har lahira a ranar 10 ga Nuwanba, 2020, a kusa da garin Filgila dake yankin Karamar hukumar Dandi a Jihar Kebbi.

Sai dai a zaman kotun a jiya, Lauyan dake tsaya wa wadanda ake kara, Barista Amina Kaoje, ta gabatar da korafinta cewa, an kai wa hukumar Kwastom takardar sammacin sauraron karar da aka sanya ranar 8 ga Maris, 2021, amma ba a ba su takardun abinda ake karar su a kai ba.

Ta kara da cewa, tun da yanzu ga ta a gaban kotun, tana neman kotun da daga sauraron karar har zuwa ranar 19 ga Maris, 2021, wanda zai ba su damar nazarin takardun karar da abubuwan ake zargin su da aikatawa, don maido da amsa ta hanyar sanya nasu takardu gaban kotun.

Shi ma lauyan mai kara, Barista Aminu Umar Kalgo, ya bayyana wa kotun cewa, “na yi mamaki idan lauyar hukumar Kwastom za ta bayyana wa kotun da cewa ba a ba su takardun karar ba, domin aikin rijistara ne ta bayyana wa kotu ko an kai wa hukumar Kwastom takardun karar da na sauraron kara ko ba a kai ba.”

Bisa ga hakan ya ce, “ba mu da wata jayayya game da rokon a dage sauraron karar har zuwa ranar 19 ga Maris, 2021.”

Lauyar hukumar Kwastom ta kara da bayyana kotun da cewa, “bisa ga yarjejeniya da amince a tsakaninta da abokin aiki, wato lauyan dake gabatar da karar, cewa, sun amince da aka dage sauraron karar har zuwa ranar 19 ga Maris, 2021, amma idan kotun ta amince da hakan, tana da damar sauraron karar a ranar da suke nema.”

A nata bangare, kotun a karkashin jagorancin Mai Shari’a Onu ya ce, kotu za ta shiga hutu a cikin kwanan. Saboda hakan zama bada lokacin da ya dace da za a dawo, don sauraren karar.

Don haka kotun ta daga sauraren karar har zuwa 16 ga Afirilu, 2021, don dawowa a cigaba da sauraren karar.

Wadanda ake karar dai sun hada da Hukumar Kwastom da shugabanta na kasa bisa zargin halaka wani matashi da jami’in hukumar ya aikata a shekarar bara.

SendShareTweetShare
Previous Post

An Karyata Shirin Kai Wa Kwalejin ‘Kanta Unity’ Hari A Kebbi

Next Post

Ranar Mata Ta Duniya: Aisha Buhari Ta Koka Kan Yawaitar Sace Dalibai Da Mata

RelatedPosts

Kwana Ɗaya Bayan Lashe Zaɓe: Shugaban Chadi Idris Deby Ya Rasu

Kwana Ɗaya Bayan Lashe Zaɓe: Shugaban Chadi Idris Deby Ya Rasu

by Sulaiman Ibrahim
8 hours ago
0

Daga Suleiman Ibrahim Bayan shekaru 31 akan mulki, Shugaban Chadi,...

Malamai

Kungiyar Malamai Ta Tallafa Wa ‘Yan Hijira Sun Shirya Taron Bita Na Ramadan

by Muhammad
13 hours ago
0

Daga Mustapha Ibrahim, Kungiyar Hada Kan zauran Malamai da kungiyar...

Zakzaky

Ramadan: El-Zakzaky Ya Raba Tallafin Abinci Ga Mabukata

by Muhammad
13 hours ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad, Shugaban harkar musulunci a Nijeriya (IMN)...

Next Post
Aisha

Ranar Mata Ta Duniya: Aisha Buhari Ta Koka Kan Yawaitar Sace Dalibai Da Mata

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version