Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Hukumar Tsaftace Muhalli A Zamfara Za Ta Samar Wa Jihar Kudin Shiga

by Tayo Adelaja
September 13, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga  Hussaini Baba, Gusau

Hukumar Tsaftace Muhali a Jihar Zamfara ta yinkuro wajan samar da hanyoyin tara kudin shiga ga jihar. Mai ba wa Gwamna Abdul’aziz Yari Abubakar shawara a hukumar, Honarabul Ibrahim Magaji Alja ne ya bayyana haka a lokacin da yake jagorantar aikin gangami na tsaftace magudanun ruwa a Gusau babban birnin jihar.

samndaads

Honarabul Ibrahim Alja ya bayyana cewa, “Hukumar ta kammala shirinta tsab don ganin jihar ta amfana da ayyukan hukumar wajen inganta tattalin arzikin jihar, don haka ta bollo da shirin gayyato kamfanoni masu zaman kansu don samar wa al’umma jihar akwatin zuba shara a gidajen da ma’aikatu sannan a rinka biyan kamfanonin, su kuma kamfanonin na biyan haraji ga  gwamnati”. Tare da cewa, “Ta irin wadannan hanyoyyin  ne kasashe da dama suka cigaba. Samar da wadannan hanyoyin hakan zai kara bunkasa tattalin arzikin Jihar Zamfara gwargwadon hali”.

Kazalika, a cewar Hon Ibrahim ka yanzu hukumar ta kashe kudade masu yawa wajen aiwatar da aikin yashe magudanun ruwa da kwalbatoci da ma fitar da wasu hanyoyin ruwa don kauce wa hadarin ambaliya da hasarar rayuka da gidaje a fadin jihar.

A karshe, Hon. Ibrahim ya nuna takaicinsa ga wadanda ba su amfani da abubuwan zuba shara a unguwanni sai su rinka zubawa a a magudanan ruwa duk da kuwa akwai shi a unguwanniin. Ya ce wannan cutar da kai ne da kuma al’umma. Daga nan sai ya yi kira ga al’ummar jihar tasu da  taimaka wajen bai wa wannan hukumar hadin kai don ganin an samu ingantatcciyar rayuwa, da kuma bai wa gwamnatin Abdul’aziz Yari hadin kai da adduo’i don ganin kudirinta ya hakaku na cigaban al’ummar wannan Jihar.

SendShareTweetShare
Previous Post

Kungiyar Dalibai Ta UDUS Sun Karrama Sarkin Keffi

Next Post

Abubuwan Kirki Suka Sa Ake Tunawa Da Sardauna – Masari

RelatedPosts

Ta’aziyar Rasuwar Sam Nda Isaiah

Sam Nda-Isaiah Ya Rasu Lokacin Da Ake Tsananin Bukatar Gudunmawarsa – Jami’ar Jos

by Sulaiman Ibrahim
22 mins ago
0

Shugabannin jami’ar Jos sun bayyana rashin jin dadinsu dangane da...

Kasuwar Mile 12

Kwamitin Da Shugaban Kasuwar Mile 12 Ya Nada Na Cigaba Da Jajanta Wa Manoman Arewacin Nijeriya

by Sulaiman Ibrahim
32 mins ago
0

Sabon kwamitin da Babban Shugaban kasuwar mile 12 Intanashinal market...

Sojoji Sun Farmaki Mahakar Ma’adanai A Zamfara, Sun Cafke ‘Yan Bindiga 150

Ranar Mazan Jiya: Babu Wani Abin Murna Ga Tabarabrewar Tsaro – Dattawa Ga Buhari

by Sulaiman Ibrahim
36 mins ago
0

Dattawan Nijeriya a karkashin inuwar gamayyar kungiyar wato (COPANE), sun...

Next Post

Abubuwan Kirki Suka Sa Ake Tunawa Da Sardauna – Masari

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version