Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RAHOTANNI

Hukumar Tsaftace Muhalli A Zamfara Za Ta Samar Wa Jihar Kudin Shiga

by Tayo Adelaja
September 13, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga  Hussaini Baba, Gusau

Hukumar Tsaftace Muhali a Jihar Zamfara ta yinkuro wajan samar da hanyoyin tara kudin shiga ga jihar. Mai ba wa Gwamna Abdul’aziz Yari Abubakar shawara a hukumar, Honarabul Ibrahim Magaji Alja ne ya bayyana haka a lokacin da yake jagorantar aikin gangami na tsaftace magudanun ruwa a Gusau babban birnin jihar.

Honarabul Ibrahim Alja ya bayyana cewa, “Hukumar ta kammala shirinta tsab don ganin jihar ta amfana da ayyukan hukumar wajen inganta tattalin arzikin jihar, don haka ta bollo da shirin gayyato kamfanoni masu zaman kansu don samar wa al’umma jihar akwatin zuba shara a gidajen da ma’aikatu sannan a rinka biyan kamfanonin, su kuma kamfanonin na biyan haraji ga  gwamnati”. Tare da cewa, “Ta irin wadannan hanyoyyin  ne kasashe da dama suka cigaba. Samar da wadannan hanyoyin hakan zai kara bunkasa tattalin arzikin Jihar Zamfara gwargwadon hali”.

Kazalika, a cewar Hon Ibrahim ka yanzu hukumar ta kashe kudade masu yawa wajen aiwatar da aikin yashe magudanun ruwa da kwalbatoci da ma fitar da wasu hanyoyin ruwa don kauce wa hadarin ambaliya da hasarar rayuka da gidaje a fadin jihar.

Ya ci gaba da cewa tuni hukumar ta samar wa al’ummar jihar abubuwan zuba shara don tara ta waje guda ta yadda lokaci bayan lokaci, motocin kwashe shara za su zagaya su kwashewa.

A karshe, Hon. Ibrahim ya nuna takaicinsa ga wadanda ba su amfani da abubuwan zuba shara a unguwanni sai su rinka zubawa a a magudanan ruwa duk da kuwa akwai shi a unguwanniin. Ya ce wannan cutar da kai ne da kuma al’umma. Daga nan sai ya yi kira ga al’ummar jihar tasu da  taimaka wajen bai wa wannan hukumar hadin kai don ganin an samu ingantatcciyar rayuwa, da kuma bai wa gwamnatin Abdul’aziz Yari hadin kai da adduo’i don ganin kudirinta ya hakaku na cigaban al’ummar wannan Jihar.

SendShareTweetShare
Previous Post

Kungiyar Dalibai Ta UDUS Sun Karrama Sarkin Keffi

Next Post

Abubuwan Kirki Suka Sa Ake Tunawa Da Sardauna – Masari

RelatedPosts

‘Goyon Bayan Da Al’ummar Fagge Suka Bamu Da Shawarar Jagororinmu Ya Sa Muka Sami Nasara’

‘Goyon Bayan Da Al’ummar Fagge Suka Bamu Da Shawarar Jagororinmu Ya Sa Muka Sami Nasara’

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

Daga Ibrahim Muhammad Kano. Sakataren mulki na karamar hukumar Fagge...

Na Sadaukar Da Albashina Ga Marayu – Ekene   

Na Sadaukar Da Albashina Ga Marayu – Ekene  

by Muhammad
3 days ago
0

Daga Abubakar Abba, dan takarar Kujerar shugaban karamar hukumar Chikun...

NAF

Martani: Babu Ragowar Jirginmu Da Ya Bace A Bama – NAF

by Muhammad
4 days ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad, An ja hankalin rundunar sojin saman...

Next Post

Abubuwan Kirki Suka Sa Ake Tunawa Da Sardauna – Masari

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version