Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Ibo ’Yan Kasuwa Sun Goyi Bayan Matakan Zaman Lafiya

by Tayo Adelaja
September 21, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Khalid Idris Doya, Bauchi

Inyamurai mazauna Jihar Bauchi sun bayyana cewar a rayuwarsu da suke yi da mutanen Bauchi babu abin da za su ce sai godiya da hamdala, domin gwamnati da al’umman jihar sun rikesu da gaskiya da kuma zaman lafiya ba tare da nuna musu wariya ba. ‘yan kabilar Ibo mazauna Bauchi wadanda suka bayyana hakan a makon jiya a sa’ilin da suka kawo zo ofishin ‘yan jarida.

samndaads

Shugaban ‘yan Kabilar Ibo mazauna Bauchi Reverend Dominic Nkwocha ya shaida hakan inda ya ci gaba da cewa “Mu Ibo mazauna Bauchi aka zamanmu a Bauchi babu abun da zamu ce sai mun gode, muna ji dadi zamanmu a wannan jihar. gwamnan jihar nan sai mu ce masa mun gode a bisa tabbatarwar da yake yi ya ga an samu zaman lafiya. Haka kuma muna jinjina wa mai martaba Sarkin Bauchi Alhaji Rilwanu Sulaiman Adamu muna jin dadin yanda yake bamu goyon baya a kowanne lokaci da kuma bamu kulawa ta musamman”. In ji shugaban na Inyamurai

Shugaban na Ibo wanda ya samu rakiyar Sakataren Kungiyar da wasu jiga-jigai sun ce Nijeriya kasa ce ta kowa ba wai na wani jinsi ba “Mun yarda Nijeriya kasarmu ce wacce Allah ya ajiye mu domin mu yi rayuwa baki daya. Kuma shi Allah da ya hada mu waje guda bai yi kuskure ba. don haka mu mun amincen da dokokin kasar Nijeriya kuma bamu da ja a kai, duk wasu matakan zaman lafiya muna na’am da su”. In ji su

Ya ce sun barranta da masu fafatukar kafa Biyafara, ya kuma yi kira da babbar murya a duk inda Inyamuri yake ya kasance mai da’a da biyayya wa dokokin kasa, “Muna fada wa duk wani Ibo a duk inda ya ke da zama, ya yi abin da ya kamata, kada ya aikata wani kuskure. Wasu mutane da suke IPOB mu bamu sansu ba; kuma bamu goyon bayansu kan abin da suke aikatawa. Don haka muka shaidawa duniya mun barranta da su”. A cewarsa

Sai ya nuna kansu a matsayin masu bin umurni da kuma dokokin zaman lafiya na Jihar Bauchi da kuma na kasa baki daya.

SendShareTweetShare
Previous Post

Wutar Lantarki: Mega Watt 2,000 Da Aka Samar Ba A Yi Tattalin Su Ba -Minista

Next Post

Wasu Amurkawa Za Su Zuba Hannun Jarin Dala Biliyan 25 A Nijeriya

RelatedPosts

APC

Zaben Kananan Hukumomi: APC Ta Kama Hanyar Lashe Dukkan Kujeru A Kano

by Sulaiman Ibrahim
1 hour ago
0

An Samu Karancin Masu Zabe An Kafa Kotun Sauraren Korafin...

Buba Marwa

Shugaban Kasa Ya Nada Buba Marwa Shugaban NDLEA

by Sulaiman Ibrahim
1 hour ago
0

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da nadin Muhammadu Buba...

Kasafin 2021

Samar Da Aikin Yi: Ministar Abuja Ta Yaba Wa Kokarin Shugaba Buhari

by Sulaiman Ibrahim
1 hour ago
0

Karamar Ministar Babban Birnin Tarayya, Dakta Ramatu Aliyu, ta yaba...

Next Post

Wasu Amurkawa Za Su Zuba Hannun Jarin Dala Biliyan 25 A Nijeriya

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version