Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

IGP Ya Ba Da Umarnin Kamo Sunday Igboho, Kan Korar Fulani Daga Oyo

by Muhammad
January 24, 2021
in LABARAI
1 min read
Rashawa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Rabiu Ali Indabawa.

Sufeto-Janar na ‘yan sanda, IGP, Mohammed Adamu, ya ba da umarnin kame Sunday Adeyemo wanda aka fi sani da Sunday Igboho, kan umarnin korar wasu Fulani da ke Jihar Oyo. Babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai, Malam Garba Shehu, ya tabbatar da hakan a wata hira da ya yi da sashen na BBC.

samndaads

Ya shaida wa BBC Hausa cewa IGP ya ba da umarni ga Kwamishinan ’Yan sanda a Jihar Oyo, Ngozi Onadeko, da ya kamo Mista Igboho ba tare da bata lokaci ba kuma a kawo shi zuwa Abuja. Idan za ku iya tunawa dan gwagwarmayar Yarbawan ya ba da sanarwar kora ga dukkan Fulani saboda zargin satar mutane da yin fashi a Igangan, Karamar Hukumar Ibarapa ta Gabas dake Jihar Oyo.

Bayan sanarwar ta kare a ranar Juma’a, Mista Igboho ya afka wa matsugunan Fulani a garin don korar Sarkin Fulanin, Salihu Abdukadir, da wasu makiyaya da ake zargi da rura wutar tsaro. Matakin na Mista Igboho ya haifar da maganganu daban-daban daga ‘yan Nijeriya, musamman a kafofin sada zumunta.

SendShareTweetShare
Previous Post

An Nada Alhaji Ummar Ibrahim Battaiya Sarautar Sai’n Gaya A Jihar Kano

Next Post

Ziyarar Kwamitin Kasuwar Mile 12 Don Jajanta Wa Manoman Jihar Kano Ya Yi Armashi

RelatedPosts

miyagun kwayoyi

Masu Garkuwa Da Mutane Muggan Kwayoyi Suke Bukata Matsayin Kudin Fansa – NDLEA

by Sulaiman Ibrahim
19 mins ago
0

Daga Idris Aliyu Daudawa Shugaba kuma babban jami’i na Hukumar...

UNICEF Ta Yi Tir Da Sace ‘Yan Matan Makaranta A Jihar Zamfara

UNICEF Ta Yi Tir Da Sace ‘Yan Matan Makaranta A Jihar Zamfara

by Sulaiman Ibrahim
43 mins ago
0

Daga Bello Hamza, Abuja Hukumar UNICEF ta bayyana damuwa tare...

Kwalejin Kimiyyar Lafiya Ta Aminu Dabo Ta Yaye Dalibai

Kwalejin Kimiyyar Lafiya Ta Aminu Dabo Ta Yaye Dalibai

by Sulaiman Ibrahim
50 mins ago
0

Daga Ibrahim Muhammad, Kano Kwalejin kimmiyar lafiya da fasaha ta...

Next Post
Mile 12

Ziyarar Kwamitin Kasuwar Mile 12 Don Jajanta Wa Manoman Jihar Kano Ya Yi Armashi

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version