INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

byYusuf Shuaibu
3 months ago
INEC

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), ta tsaida ranar 16 ga Agusta don gudanar da zabe cike gibi a mazabe 16 da ke a jihohi 12 na tarayyar Nijeriya.

Hukumar ta kara da cewa za ta tura jami’ai 30,451 don gudanar da zaben, kuma ta sanar da ci gaba da yin rajistar zabe a duk fadin kasar, daga ranar 18 ga watan Agusta.

  • Sin Ta Bai Wa Habasha Kayayyakin Tallafin Jinya
  • Ɗan Wasan Liverpool, Diogo Jota, Ya Mutu A Hatsarin Mota

Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, wanda ya bayyana wannan a taron tattaunawa tare da jam’iyyar siyasa a Abuja, ya ce bisa ga korafe-korafen da ke fitowa daga jam’iyyun adawa na cewa wadanda suka dade suna rike da mukamai sukan hana su samun damar amfani da wuraren gwamnatin, ciki har da kafofin watsa labarai na gwamnati.

Ya ce daga yanzu, hukumar za ta yi aiki tare cibiyar hadakar jam’iyyu (IPAC) da hukumar kula da tallace-tallace ta Nijeriya (ARCON), don daukar matakin shari’a kan masu irin wannan laifi.

Yakubu ya ce, “Yayin da ake fara ayyukan yakin neman zabe a Jihar Anambra, ina so in jawo hankali ga masu korafe-korafe musamman jam’iyyun adawa game da Rashin bayar da damar shiga wuraren gwamnati don gudanar da ayyukan zabe. Wadannan sun hada da kafofin yada labarai na jihar, gine-ginen gwamnati don taruka da kuma wuraren da ake kibe don yin gangamin da taruka.”

“A wasu lokutan, ana cajin kudi masu yawa waje tallace-tallace. Wadannan abubuwan na cikin rashin bin doka a cikin dokar zabe ta 2022 wadda ke hana amfani da matsayi don musguna wa kowanne jam’iyya ko dan takara.

“Hukumarmu za ta yi aiki tare da cibiyar hadakar jam’iyyu (IPAC), kuma za mu kara karfafa hadin gwiwarmu da hukumar kula da tallace-tallace ta Nijeriya (ARCON), don daukar matakin doka idan aka samu shaidu masu karfi na karya doka.

“Game da zaben cike gibi kuwa, bari in ba ku takaitaccen bayani kan lamarin. A cikin shekaru biyu da suka gabata tun lokacin kaddamar da majalisun kasa da na jihohi a watan Yunin 2023, an samu kujerun ‘yan majalisa da babu kowa wanda ake bukatar yi zabe a fadin kasar nan.

“Idan za ku iya tunawa cewa a watan Fabrairu na shekarar da ta gabata, hukumar ta gudanar da zaben cike gurbi domin cike kujeru guda tara da aka samu sakamakon mutuwar ko murabus na ‘yan majalisun tarayya na jihohi. Tun daga wannan lokacin, an samu karin gurabe a fadin kasar nan.

“A saboda haka, hukumar ta fitar da ranar Asabar, 16 ga Agusta, 2025, don gudanar da zaben cike gibi a mazabu 16 a da ke jihohi 12 na kasar nan, wanda ya kunshin adadin masu zabe 3,553,659 da aka yi wa rajista, wanda aka rarraba a cikin kananan hukumomi 32, wuraren zabe 356 da kuma rukunin zaben 6,987. Hukumar za ta tura jami’ai 30,451,” in ji shugaban INCE.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version