INEC Ta Goge Sunayen Matattu 7,746 Daga Rajistar Zabe
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

INEC Ta Goge Sunayen Matattu 7,746 Daga Rajistar Zabe

byYusuf Shuaibu
9 months ago
INEC

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta sanar da cewa an cire sunayen matattun masu kada kuri’a har guda 7,746 daga rajistar masu zabe a jihohi 36 da kuma Babban Birnin Tarayya Abuja a zuwa watan Disambar 2022.

Daraktar wayar da kan jama’a da masu kada kuri’a, Bictoria Etta-Messi ce ta bayyana hakan ga manema labarai.

  • A Shirye Kasar Sin Take Ta Kyautata Dangantakar Tattalin Arziki Da Amurka
  • Shirin Tallafinmu Ga Nijeriya A 2025 Zai Kai Ga Asalin Mabukata – Wakilin MDD

“Mutane dubu bakwai da dari bakwai da arba’in da shida sun ragu a fadin jihohi 36 da kuma Babban Birnin Tarayya Abuja daga rajistar masu kada kuri’a zuwa watan Disamba 2022,” in ji ta.

A cewar hukumar INEC, ana tsaftace rajistar masu kada kuri’a kafin kowane babban zabe.

A bitar zaben 2023 bayan kammala zabe a watan Disamba na 2024, INEC ta bayyana kalubalen da ke tattare da tsaftace rajistar masu kada kuri’a, duk da ingantuwar tsarin rajistar masu kada kuri’a da aka samu wanda ya kara sabbin masu rajista har guda 12,298,944.

Wani babban batu shi ne, wahalar cire wadanda suka mutu sakamakon gibin bayanan mutuwar a hukumance.

“Matsalolin da ke tattare da bayanan mutuwar jami’ai na ci gaba da yin wahala ga INEC wajen cire wadanda suka mutu rajistar zabe,” in ji hukumar.

Hukumar ta kuma gano matsalar yin rajista sau biyu ko kuma da yawa, wanda aka magance ta hanyar tura na’urar tantance bayanan masu kada kuri’a.

Wannan tsari ya ba da alama tare da cire shari’o’in 2,780,756 na rajista marasa inganci, wanda ke wakiltar kashi 22.6 na duk sabbin masu rajista a fadin kasar nan.

INEC ta kara nuna damuwa game da raguwar fitowar masu kada kuri’a. Zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar dokokin kasar a shekarar 2023, ya samu fitowar kashi 27.5 cikin 100, inda ya ragu da kashi 35.6 a shekarar 2019.

Wasu masu ruwa da tsaki sun alakanta wannan raguwar wani bangare na hauhawar rajistar masu kada kuri’a tare da yin kira da a kara himma wajen tsaftace ta.

Masu ruwa da tsaki a wannan bitar sun ba da shawarar cewa ya kamata INEC ta karfafa hadin gwiwa da hukumomi irinsu hukumar kula da yawan jama’a ta kasa (NPC) da kuma hukumar kula da tantance ‘yan kasa (NIMC) domin tantance wadanda suka mutu.

Akwai kuma kiraye-kirayen a dakatar da mutanen da ba su yi zabe ba a zabuka uku da suka gabata da kuma bukatar su sake sabunta rajistarsu.

“Shawara daya daga cikin wannan bita ita ce a karfafa hadin gwiwa da sauran hukumomi irinsu NIMC da NPC don zakulo wadanda suka rasu a cikin rajista da cire su. Bugu da kari, hukumar za ta iya dakatar da mutanen da ba su yi zabe ba a zabuka uku da suka gabata daga rajistar tare da neman su sabunta rajistarsu,” in ji INEC a bitarta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda, Sun Kama Masu Safarar Makamai, Sun Ceto Mutane

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version