Hussaini Yero">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

INEC Za Ta Kammala Zaben Dan Majalisa Yau A Zamfara

PDP Da APC Na Zargin Juna Da Kawo Cikas

by Hussaini Yero
December 9, 2020
in RIGAR 'YANCI
3 min read
Zaben Dan Majalisa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta bayyana cewa, za ta sake zaben cike gurbi na dan majalisar tarayya a Jihar Zamfara yau Laraba, bayan da hukumar ta soke zaben sakamakon aringizon kuri’u da a ka yi da kuma satar akwatinan zaben.

Sai dai kuma tsohon Gwamnan jihar ta Zamfara, Hon. Abdul’aziz Yari, ya yi barazanar cewa, jam’iyyar APC ba za ta shiga zaben da za a yi a yau din ba, wanda hukumar ta soke idan har ba a tabbatar da tsaro ba.

samndaads

Yari ya bayyana haka ne a lokacin da ya ke ya zantawa da manema labarai bayan taron masu ruwa da tsaki na APC da ta gudanar a gidansa da ke Talata Mafara.

Tsohon Gwamnan ya zargi Gwamna Bello Mohammed Matawalle na Jihar Zamfara da manyan ma’aikatan gwamnatin jihar da hada baki da wasu jami’an tsaro, don murde zaben ta hanyar goyon bayan Jamiyyarsa ta PDP.

Yari ya kuma zargi kwamishinan kudi, Alhaji Rabiu Garba, da na Kananan Hukumomi da Cigaban Al’umma, Alhaji Yahaya Chado, da Kwamishinan Aikin Gona, Dr. Yarkofoji, da kwace akwatin zabe a lokacin zaben, wanda a ka bayyana a matsayin wanda bai kammala ba.

Tsohon gwamnan ya ce, idan har jami’an tsaro ba su tsara abubuwan da za su tabbatar da tsaron wakilan APC da magoya bayansu ba, jam’iyyar ba za ta jefa rayukan wakilanata da magoya bayanta cikin hadari ba a zaben na Laraba.

“Abinda ya faru a ranar Asabar ba za a iya bayyana shi a matsayin zabe ba, amma abin kunya abin takaici ne matuka cewa jami’an tsaro, wadanda ya kamata su tabbatar an gudanar da zaben cikin lumana, su ne wadanda ke ba da goyon baya da goyon bayan manyan ma’aikatan gwamnati da wakilan PDP wajen kwace akwatunan zabe.

“Don haka idan jami’an tsaro ba su dauki gagarumin mataki ba, don kauce wa abinda ya faru a ranar Asabar ba, to za mu janye ba za mu shiga zaben ba,” in ji Yari.

Haka kazalika, Jamiyyar PDP reshen jihar Zamfara ta nuna kaduwarta kan kalaman da jami’in tattara sakamakon zaben, Farfesa Ibrahim Magawata, ya yi yayin a zaben maye gurbin da ya gabata a jihar.

“Kuma mu ba mu gamsu ba da Farfesa Magawata a kan jagorancin gabatar da zaben a gobe laraba da za’a gabatar,” in ji ta.

Da ya ke jawabi a taron manema labarai a Gusau, Shugaban Kwamitin PDP kan zaben Bakura, Sanata Lawal Hassan Dan’Iya, ya koka kan cewa jami’in tattara sakamakon ya nuna bangaranci. A lokacin bayanin jami’in tattara sakamakon zaben na hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) a zaben maye gurbin ranar Asabar din da ta gabata a Mazabar Bakura ta jihar Zamfara, Farfesa Ibrahim Magatawa ya nuna bangaranci wajan fadi sakamakon zaben,” in ji Dan’Iya.

“Kuma tsafin ‘Yan majalusun tarayya irin su Sani Jaji da Abudulmalik Zanna da Kwamishinonin tsohon Gwamna Yari, sun taka rawa wajan ganin sun yi magudin zabe da amfanin da ’yan ta’adda, don kawo wa zaben cikas,” in ji Sanata Dan’Iya.

“Duk mai kaunar dimukradiyya ya yi Allah-wadai da dabi’un APC wajen daukar ’yan daba, musamman daga yankin Zuru na Jihar Kebbi ta su ka kawo su a mazabar, Dakko da Damri wadanda da gangan suka zo ba tare da son rai ba su ka tayar da rikici a lokacin zaben.

“Babban damuwarmu shi ne yadda a ka yi amfani da jami’ai cikin kaki, don kare munanan ayyukan masu karya doka. Mu na matukar damuwa yadda wasu jami’an tsaro su ka kauda kai daga ayyukan ‘yan baranda su ka cigaba da bayar da kariya ga su ‘yan ta’adan,” in ji shi.

Sanata Daniya ya ce duk da soke zabe a rumfunan zabe 14, PDP ta lashe zaben gabadaya ba za mu karaya ba a zaben gobe kuma gaskiya za ta yi halin da da yardar Allah APC, sai ta kunyata a zaben.

SendShareTweetShare
Previous Post

Korona: Gidauniyar BUA Ta Tallafa Wa Bauchi Da Motoci Da Kyallen Hanci

Next Post

Sanata Yahaya Abdullahi Ya Ja Kunnen Matasa Su Kasance Jakadu Nagari

RelatedPosts

Ingantaccen zabe

Aniyar Ganduje Ce Ta Haifar Da Ingantaccen Zabe A Kano – Yusif Ali

by Hussaini Yero
12 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana cewa, kyakkyawar aniyar Gwamna...

Kaduna

Sojoji Sun Yi Wa ‘Yan Bindiga Kwanton Bauna A Kaduna

by Hussaini Yero
12 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Sojojin da ke karkashin ‘Operation Thunder...

Farar Hula

Hankula Sun Tashi A Maiduguri Bayan Babbaka Sojan Da Ya Harbi Farar Hula Hudu

by Hussaini Yero
12 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Mutanen Maiduguri sun shiga tararrabi bayan...

Next Post
Sanata Yahaya Abdullahi

Sanata Yahaya Abdullahi Ya Ja Kunnen Matasa Su Kasance Jakadu Nagari

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version