Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home HANTSI

Irin Matar Da Ya Kamata A Aura

by Sulaiman Ibrahim
March 12, 2021
in HANTSI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Kafin mutum ya yanke shawarar yin aure ya kamata ya bi matakai guda uku, na farko ya yi istikharah wato neman zabi daga wurin Allah, kamar haka; da fari mutum zai yi Sallah raka’a biyu kamar yadda ya zo a Hadisi, bayan ya yi sallama (wasu malamai suna ganin za a iya yin wannan addu’a kafin sallama), wato addu’ar neman zabi daga Allah, ko kuma mika wa Allah lamarin.

Mataki na biyu. Ya nemi shawara daga masana addini da dabi’u da halayya da gogayya da harkokin aure, domin su ba shi shawara bayan sun saurare shi sun ji irin tasa bukatar, wanda yake shawara ba zai yi nadama ba.
Mataki na uku.
Dole mai neman aure mace ko namiji su cire son zuciya idan su na neman aure nagari, duk da shari’a ba ta yarda mutum ya auri matar da baya so ba, amma mafi yawan mata na gari ba su fiya kyau da yawa ba, said ai hakan ba ya nuna cewar babu matar kirki a kyawawa, don haka idan an samu mace mai kyau amma ba ta da tarbiyya, sai kuma aka samu mai riko da addini kuma mai tarbiyya kuma tana da karancin kyau, sai ka ga an raba hankalin mai neman aure.
Ana auren mace saboda abu hudu, na farko; saboda kyawunta, na biyu saboda kudinta, na uku saboda nasabarta, na hudu saboda addininta.
Ma’akin Allah ya ce zai fi kyau ka auri ma’abociyar addini, idan ka ki hannun ka ya yi turbaya.
Wadannan abubuwa guda hudu su ne mafi yawan masu neman aure suka fi bukata ga mace, amma ana samun wata ta hada dukkan wadannan suffofin, wata kuma ta sami uku daga ciki, wata ta sami biyu wata ma suffa daya kawai take da ita daga cikin wadannan siffofin.

Wacce ta fi ita ce wacce ta hada dukkan wadannan suffofin:
– Mai kyau, mai kudi, mai nasaba, mai addini dukkan hudun tana da shi.
– Mai addini da kyau.
– Mai matsayi da kudi amma babu kyau babu addini.
– Mai addini amma babu kudi.
– Kyakkyawa amma babu tarbiyya ta addini.
– Mace tana da suffofi guda biyu na fili kamar kyau da muni ko baki da fari ko tsawo da gajarta, a kwai kuma suffofi na boye kamar kirki da hakuri da tarbiyya da juriya da iya zaman aure.

Mafi yawan mutane sun fi son mace mai kyau, hakan kuwa ba laifi bane, amma idan mutum ya auri mace saboda kyawunta kawai, lokacin da kyawun ya tafi, sai ka ga mace tana samun canji daga mijinta, saboda abin da ake son ta saboda shi ya tafi ko ya kare kuma mace mai kyau kawai babu tarbiyya sun fi wahalar da mazansu da halakar da su, domin za su rika yin abin da bai kamata ba.

A wasu lokuta domin su faranta musu ko da hakan ya sabawa Allah da Manzonsa.
Kowa cikin masu neman aure daga cikin maza ko mata akwai suffofin na fili da yake sha’awa daga matar da yake so ya aura, ko daga mijin da take so ta aura, kamar fara ko baka, doguwa ko gajeriya, mai kiba ko siririya, kyakkyawa ko mummuna, amma shi kyau da muni ya dangana ne da abin da mutum yake so, domin mummuna a wajen wani kyakkyawa ce, kuma kyakkyawa a wajen wani mummuna ce.

Mace mai tarbiyya de ita ce abin nema, idan ka samu mai tarbiyya kuwa ka gama more rayuwar aure.

SendShareTweetShare
Previous Post

Wasan Golf A Switzerland Ta Hanyar Tsaunuka Da Abubuwan Al’ajabi

Next Post

Matar Da Ba Ta Sana’a Ko Wurin Miji Ba Ta Da Martaba – Khadija Sharubutu

RelatedPosts

Jigawa

Kashi 90 Na Masu Bautar Kasa A Jigawa Za Su Karantar A Makarantun Yankunan Karkara

by Muhammad
1 day ago
0

Hukumar kula da masu bautar kasa (NYSC) reshen Jihar Jigawa...

Soyayyar Zamani

Shawara Zuwa Ga Ma’aurata Masu Husuma Da Masu Niyar Aure

by Sulaiman Ibrahim
2 weeks ago
0

Babu shakka da yawa daga cikin ma'aurata suna samun husuma...

Auren Da Nake Muradi

Auren Da Nake Muradi

by Sulaiman Ibrahim
4 weeks ago
0

Matasa wannan sashi ne na musamman da muka kirkiro muku...

Next Post
Matar Da Ba Ta Sana’a Ko Wurin Miji Ba Ta Da Martaba – Khadija Sharubutu

Matar Da Ba Ta Sana’a Ko Wurin Miji Ba Ta Da Martaba - Khadija Sharubutu

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version