Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home KASASHEN WAJE

ISIS Ta Hallaka Mutane 74 A Iraki

by Tayo Adelaja
September 16, 2017
in KASASHEN WAJE
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Akalla mutane 74 ne suka rasa rayukansu wani kazamin harin bom da bindiga da aka kai kusa da birnin Nasiriyah da ke kudancin Iraki. Haka zalika da dama sun samu raunuka a harin wanda kungiyar IS ta dauki alhakin kai wa.

Mataimakin shugaban sashen kiwon lafiya na lardin Dhikar da ke birnin Nasiriyah, Abdel Hussein Al-Jabri, ya shaidawa Kamfanin dilancin Labaran Faransa na AFP, cewa yanzu haka akwai sama da mutane 87 da suka samu munanan raunuka a harin bayan wadanda suka rasa rayukansu.

samndaads

Haka kuma ya bada tabbacin cewa akwai yiwuwar adadin wadanda suka mutun ya karu nan da wani lokaci idan aka yi la’akari da munanan raunukan da suka samu.

Al-Jabri ya kuma bayyana cewa yanzu haka zaman lafiya ya fara dawowa yankin da lamarin ya faru, bayan da aka kwashe gawakin majinyatan kuma aka garzaya da su asibitoci don karbar kulawar gaggawa.

Bama-bamai Sun Tashi A Kasar Ingila

Wasu tagwayen bama-bama sun tashi a birnin Landan na kasar Ingila, sai dai babu rahoton mutuwar mutane, amma mutane akalla 22 sun ji munanan raunuka.

Fira ministar Britaniya, Theresa May ta ce za a ci gaba da karfafa tsaro a kasar sakamakon harin da aka kai wanda ya yi sanadiyar raunata mutane akalla 22.

Rundunar ‘yan sanda a Britaniyan ta ayyana harin a matsayin na ta’addanci inda ta shawarci al’umma da su guji zuwa wurin da aka samu fashewar da ta haifar da rud

ani a tashar jirgin a ya yin bincike gano wadanda suka kai wannan harin.

Magajin garin birnin Landan Sadik Khan a jawabinsa ga manema labarai bayan aukuwar lamarin ya yi alla-wadai da abinda ya kira ayyukan muggan mutane da ke amfani da ta’addanci domin hana al’umma walwala, karo na biyar kenan da ake kai wa Britaniya hari a cikin wannan shekara ta 2017.

SendShareTweetShare
Previous Post

Kasuwancin ’Yan Nijeriya Na Bunkasa A Afirka Ta Kudu

Next Post

Hadarin Jirgin Ruwa Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum 20 A Kasar Indiya

RelatedPosts

Amurkawa

Biden Ya Gabatar Da Shirinsa Na Yi Wa Dukkan Amurkawa Rigakafi

by Sulaiman Ibrahim
3 days ago
0

Zababben shugaban Amurka Joe Biden ya gabatarwa Amurkawa shirinsa na...

Jamhuriyar Afrika

Yawan ‘Yan Jamhuriyar Afrika Ta Tsakiya Da Ke Gudun Hijira Ya Ninka Cikin Mako Daya

by Sulaiman Ibrahim
3 days ago
0

Majalisar Dinkin Duniya ta ce adadin ‘yan gudun hijirar dake...

Masu Neman Mafaka Sun Fara Tattaki Daga Honduras Zuwa Amurka

by Sulaiman Ibrahim
4 days ago
0

Wani sabon ayarin dubunnan masu neman mafaka a Honduras sun...

Next Post

Hadarin Jirgin Ruwa Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum 20 A Kasar Indiya

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version