Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Iya Jajircewar Da Ka Yi APC Ta Hau Mulki Iya Wuyar Da Kake Sha Yanzu – Bishir Biro Kankia

by Tayo Adelaja
September 18, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga El-Zaharadeen Umar,  Katsina

Wani Matashin dan siyasa a karkashin jam’iyyar PDP a jihar Katsina mai suna Alhaji Bishir Biro Kankia ya bayyana cewa gwargwadon yadda ka taimakawa jam’iyyar APC ta dare karagar Mulki to gwargwadon yadda kake shan wuya a wannan lokaci.

samndaads

Bishir Biro Kankia ya yi wannan furucin ne a lokacin da ake tattaunawa da shi a gidan bision FM Rediyon Katsina a cikin shirinsu na kowane tsuntsu… wanda kuma haka yana daga cikin martani da ya mayar wa ‘ya ‘yan jam’iyyar APC da suke cewa PDP ta yi barna a cikin shekaru 16 da ta yi tana mulki.

Inda ya bayyana wasu ayyuka da suka yi tare da kalubalantar ma su cewa barna jam’iyyarsu ta tabka a lokacin da suke kan mulki. Wasu daga ayyukan da ya bayyana sun hada da Biyan kudin jarabawa da gina baban titin da ya kewaye garin Katsina da gina sabon gidan Gwamnati da gina jami’ar Umaru Musa Yar’adua da gida Asibitin kashi da gina filin sauka da tashin jirage da gina Babban filin wasa da kuma sakatariya gwamnatin jihar Katsina.

Ya kuma kara bayyana dalilinsa na cewa gudumawar da ka bada ita gwargwadon wuyar da kake sha, ya ce lokacin Jonathan kudin Hajji dubu dari bakwai yanzu miliyan da rabi kudin Man fetur 86 yanzu 145, ya kara da cewa da Jonathan ne yake mulki kuma ya kara wadannan kudadan da har gida za a bi su ana jifa amma yanzu ga shi Musulmi ne ke Mulki amma an yi shiru.

Mu da ake ganin idan jam’iyyar APC ta hau mulki za a yi wa rigunar gamin baki  za mu saki matanmu saboda wuya to yanzu duk inda ka ga mutum da komari yana da kwanciyar hankali to dan PDP ne, inji Bishir Biro.

Ya kara cewa  babban abinda ya burgeshi game da wannan mulki na jam’iyyar APC shi ne malamai wadanda suka rika shiga Masallaci suna kafirtasu idan sun tafi zabe suna yi masu kabbara, yau sai gashi ana musayar wuta tsakanin wadannan Malamai da gwamnatin su da aka ce ba mu da tsarki suna da najasa.

SendShareTweetShare
Previous Post

An Kafa Kwamitin Da Zai Sa Ido Kan Hakar Ma’adanai

Next Post

Kungiyar NURTW Ta Kaddamar Da Sabbin Shugabanni A Galma

RelatedPosts

Makiyaya Ondo

Korar Makiyaya A Ondo: Cikakken Rahoton Yadda Ta Kaya Taron Gwamnoni Da Shugabannin Fulani

by Muhammad
20 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya, Gwamnonin Nijeriya sun kira taron gaggawa...

Kasafin 2021

Hotunan Sabbin Shugabannin Rundunonin Tsaro

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Major-Gen. Leo Irabor, Chief of Defence...

Garban

Garban Kauye Farawa Ne Allurar Dinke Barakar Kumbotso – Muslihu Yusuf Ali

by Muhammad
3 days ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana zaben Sabon shugaban Karamar...

Next Post

Kungiyar NURTW Ta Kaddamar Da Sabbin Shugabanni A Galma

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version