Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Iyaye Ku Rage Buri Kan Auren ’Ya’yanku Mata – Ustaz Tijjani Sarkin Noma

by Muhammad
December 29, 2020
in RIGAR 'YANCI
2 min read
'Ya'yanku
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Ahmed Muh’d Danasabe,

 

samndaads

An yi kira ga iyaye, musamman mata dasu rage buri da kuma son abin duniya a yayin da aka zo neman yayansu mata da aure.

Wani malamin addinin musulunci dake garin Lokoja, babban birnin jihar Kogi, Ustaz Ahmad Tijjani Sarkin Noma ne yayi kiran a wajen walimatu Nika’in auren Mallam Abdullahi Abubakar Sha’aban da amaryarsa, Malama Khadijat Aliyu Abdullahi Dan Sokoto da kuma Mallam Abdulsalam Sha’aban da amaryarsa, Malama Khadijat Uthman  wanda aka gudanar a gidan babban limamin garin Lokoja dake Unguwar Fawa a ranan Asabar data gabata.

Ustaz Ahmad Tijjani Sarkin kazalika ya bayyana cewa yawan zinace zinace na faruwa a tsakanin saurayi da budurwansa ne idan har suka dauki lokaci mai tsawo ba suyi aure ba saboda tsadar da auren ke da shi, wadda hakan a cewar malamin shike haifar da haihuwar shegu barkatai, lamarin dake haddasa masifu iri iri a doron kasa.

Ya kara da cewa” Zaka ga mutum jarinsa bata wuce naira 500,000 ba, amma Kuma sai kaga iyayen yarinya, musamman mata wai don yaje neman auren yarsu, sai su zayyano masa abubuwan da yafi karfinsa. A don haka nake shawartan iyaye mata da ku duba irin yanayin halin da ake ciki a wannan zamani na matsin tattalin arziki,ku rika sassautawa duk wanda yazo neman diyarku da aure. Ku rage yawan buri da son abin duniya a yayin da aka zo neman yayanku mata da aure. Ina mai tunatar da ku cewa aure mafi albarka shine auren da aka kashe dukiya mafi kankanta kamar yadda Annabi Muhammadu ( SAW) ya fadi”Inji Usta Tijjani Sarkin Noma.

Malamin har ila yau ya shawarci namiji mai  neman aure da ya guji nuna karya ga yarinya ko iyayenta a yayin da  neman aurenta,inda yace yin haka yana daya daga cikin abubuwan dake rusa auren koda an samu nasarar yinta,yana mai cewa karya fure take bata yaya.
A karshe Ustaz Ahmad Tijjani Sarkin Noma yayi wa angwaye da amarensu fatan samun zaman lafiya mai dorewa tare da yin kira gare su dasu suyi hakuri da junansu  cikin zamantakewar auren.

SendShareTweetShare
Previous Post

Masu Sukar Manufofin Gwamnatina Kauyawa Ne – Ganduje

Next Post

Yadda Sarkin Koton Karfe Ya Nada Wa Mutum 37 Sarautu

RelatedPosts

Ingantaccen zabe

Aniyar Ganduje Ce Ta Haifar Da Ingantaccen Zabe A Kano – Yusif Ali

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana cewa, kyakkyawar aniyar Gwamna...

Kaduna

Sojoji Sun Yi Wa ‘Yan Bindiga Kwanton Bauna A Kaduna

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Sojojin da ke karkashin ‘Operation Thunder...

Farar Hula

Hankula Sun Tashi A Maiduguri Bayan Babbaka Sojan Da Ya Harbi Farar Hula Hudu

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Mutanen Maiduguri sun shiga tararrabi bayan...

Next Post
Sarautu

Yadda Sarkin Koton Karfe Ya Nada Wa Mutum 37 Sarautu

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version