Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home JAKAR MAGORI

Jami’an Tsaro Sun Damke Dan Shakara 10 Kan Fashi Da Makami

by Muhammad
February 18, 2021
in JAKAR MAGORI
2 min read
Fashi
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Jami’an tsaro sun kama wani karamin yaro dan shekara 10 kacal mai suna Monday Omoruye, wanda ke zaune a titin Ring Road da ke Jihar Edo, saboda shigarsa cikin ayyukan aikata laifin da aikata ya hada da fashi da makami.

A cikin wani faifan bidiyo wanda yanzu ya yadu a yanar gizo, Monday ya bayyana cewa, dan uwansa ne ya sanya shi a harkar fashi, kuma zuwa yanzu ya gudanar da ayyukan fashin sau hudu.

samndaads

Lokacin da aka tambaye shi daga ina ya samo makamansa, sai ya ce yayin zanga-zangar #EndSARS na shakarar 2020, shi da dan uwansa da wasu abokansu sun kutsa kai ofishin ’yan sanda na kasuwar Oba inda suka yi awon gaba da makamai daga ofishin.

Da yake ci gaba da magana, Monday ya ce, dan uwan nasa ya koya masa yadda ake harbi da bindiga, kuma zuwa yanzu ya kashe mutane biyu a yayin da suke aiwatar da wani fashi.

“Akwai wani mutum, ban sani ba ko ya buge yake, ya ba mu wayarsa, muka mayar da ita. Ya fadawa dayan mutumin cewa yana son barci, sai muka ce masa kar ka barshi ya yi barci saboda wancan zai saci komai, kudi da wayoyi, mutumin bai saurara ba. Lokacin da gari ya waye ne na ce kar ku ba shi wayarka, amma bai saurara ba, dayan ya ce masa yana son saukar da wakoki da yawa a wayar, amma ya gudu don haka muna nemansa, kuma mai wayar ya ce idan ba ya ganinsa, zai rike ni, shi ya sa ya rike ni, ya kira min ‘yan banga. Yayana yana da bindigogin ‘yan sanda guda biyu da ya sace daga ofishin ‘yan sanda a kasuwar Urban yayin zanga-zangar #EndSARS,” in ji Monday.

Ya ci gaba da cewa, “Zan iya amfani da karamar bindiga, dan uwana ya koya min kuma yana rike su duka. Na bi su har sau hudu yin fashi a Sapele, hanyar Siluko, Sakpoba. Mun kashe mutane 2, daya a hanyar Siluko, dayan kuma a Kasuwar Igan. Ban san sunayen wadanda muka kashe ba, domin da mungama fashi muke guduwa. Idan yana son ganin dan uwana, sai an tafi da safe da misalin karfe 8 na safe, za a ganshi.”

SendShareTweetShare
Previous Post

Abubuwa Tara Da Suka Kamata A Sani Game Da Cutar ‘Hepatitis C’

Next Post

’Yan Sanda Sun Kama Wani Mutum Da Sassan Jikin Mutane A Osun

RelatedPosts

Yadda Wasu Tsoffin Fursunoni Suka Sake Tafka Ta’asa

Yadda Wasu Tsoffin Fursunoni Suka Sake Tafka Ta’asa

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

Daga Mahdi M Muhammad A ranar Litinin da ya gabata...

An Damke Wani Dan Fashi A Nasarawa

An Damke Wani Dan Fashi A Nasarawa

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

Daga Mahdi M Muhammad Kakakin rundunar, ASP Ramhan Nansel, ya...

Makanike

Wani Mutum Ya Soke Makwabcinsa Da Kwalba

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

Daga Mahdi M Muhammad Rundunar ‘yan sandan reshen jihar Legas...

Next Post
Sassan Jikin

’Yan Sanda Sun Kama Wani Mutum Da Sassan Jikin Mutane A Osun

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version