Jami'ar Bayero Ta Shirya Bikin Yaye Ɗalibai Karo Na 39
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar Bayero Ta Shirya Bikin Yaye Ɗalibai Karo Na 39

byNaziru Adam Ibrahim
8 months ago
Bayero

Jami’ar Bayero ta Kano (BUK), ta shirya gudanar da bikin yaye ɗalibai karo na 39 daga Laraba, 12 ga Fabrairu, zuwa Asabar, 15 ga Fabrairu, 2025 inda dubban ɗalibai za su karɓi takardun shaidar kammala karatu, tare da bayar da digirin girmamawa.

Shugaban jami’ar, Farfesa Sagir Adamu Abbas, ne ya sanar da hakan a taron manema labarai da aka gudanar a ranar Litinin, inda ya bayyana cewa a ranar farko, ɗalibai 4,404 za su karɓi takardun shaidar kammala karatu na digiri da difloma.

  • Kotu Ta Dakatar Da Yunkurin Aminu Ado Bayero Na Gyaran Fadar Nassarawa
  • Binciken Jami’ar Bayero Ya Gano A Hoton Yatsa Za A Iya Gane Mai Cutar Daji – Farfesa Darma

A rana ta biyu kuma za a yaye wasu ɗalibai 4,367 daga sassa bakwai na jami’ar, ciki har da 176 masu shaidar Digirin daraja ta Farko (First Class), da 2,590 masu digiri na biyu da kuma 275 masu digirin digirgir (Ph.d), sai kuma 535 masu Diflomar gaba da digiri Digiri (Postgraduate Diploma).

Kazalika za a gabatar da lakcar yaye ɗalibai, wacce Khalil Sulaiman Halilu, Mataimakin Shugaban NASENI, zai gabatar da kuma Ministan Kimiyya da Fasaha da Ƙirkire-Ƙirkire, Chief Uche Jeoffrey Nnaji, wanda shi ne zai shugabanci taron, inda jigon lackcar shi ne: “Ƙirkire-Ƙirkire da Kasuwanci: Hanyar Samar da ci gaban ƙasa.”

A ranar ƙarshe na bikin jami’ar za ta karrama wasu fitattun mutane da Digirin Girmamawa, ga Colonel Sani Bello, mai ritaya da Alhaji Auwalu Abdullahi Rano, duba gagarumar gudunmawar da suka bayar ga al’umma, haka kuma za a naɗa Farfesa Garba Dahuwa Azare, da Farfesa Julius Afolabi Falola, da Farfesa Musa Mohammed Borodo da matsayin Farfesoshi Masu Darajar (Emeritus) saboda gudunmawarsu a fagen ilimi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta
Ilimi

Minista Nnaji Ya Yi Ƙarar Jami’ar UNN Kan Rikicin Takardun Kammala Makaranta

October 6, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya
Ilimi

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet
Ilimi

Jami’ar Ibadan Ta Bude Sashen Karatu A Gida Ta Intanet

October 4, 2025
Next Post
Ɗan Majalisar Wakilai Daga Kaduna Ya Sauya Sheka Zuwa APC

Ɗan Majalisar Wakilai Daga Kaduna Ya Sauya Sheka Zuwa APC

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version