Jami'ar Franco-British International Ta Shirya Soma Aiki A Watan Oktoba – Shugaban Jami’ar
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar Franco-British International Ta Shirya Soma Aiki A Watan Oktoba – Shugaban Jami’ar

byBello Hamza
1 year ago
Franco

Jami’ar Franco-British International University a Kaduna, jami’a ce irinta ta farko a Nijeriya da take da salon koyarwa na Birtaniya da Faransa, ta shirya soma fara ayyukan ilimi a watan Oktoban 2024.

Hakan ya fito ne a wata tattaunawa da shugaban jami’ar, Farfesa Abdullahi Muhammad Sabo da manema labarai a ranar Litinin.

  • Gwamnati Ta Janye Dokar Hana Fita A Kaduna Da Zariya 
  • Yadda Mahara Suka Jefa Bam A Ofishin Jami’yyar APP A Ribas

A cewar shugaban jami’ar, jami’ar za ta fara ne da makarantu uku, wato; makarantun Kwamfuta (Computing), Jinya (Nursing), da Kimiyyar Lafiya (Health Sciences).

Farfesa Adamu Abubakar Gwarzo ne ya kafa Jami’ar Franco-British International University, wanda kuma shi ne ya kafa Jami’ar Maryam Abacha American University ta Nijeriya da ta Nijer (MAAUN) da kuma Jami’ar Canada da ke Abuja.

Har ila yau, wanda ya kafa jami’ar, Farfesa Adamu Gwarzo, a wata sanarwa da ya fitar a lokacin ziyarar shugaban jami’ar tarayya ta Dutsin-Ma (FUDMA), Farfesa Armayau Hamisu Bichi, ya nanata kishinsa da jajircewarsa kan harkar ilimi, inda ya ce zai bai wa fannin dukkanin gudummawar da ya kamata.

Ya lurantar da cewa a Nijeriya, “Jami’ar Franco-British International University (FBI) wani yunƙuri ne na fitar da ingantaccen ilimi a Afirka.”

Hukumar Kula da Jami’o’i ta Kasa (NUC) ta ba Jami’ar Franco-British International lasisin aiki a shekarar 2023 tare da Jami’ar Canada ta Nijeriya, wacce kuma ke cikin rukunin jami’o’in MAAUN.

“An san ni kan ilimi kuma zan ci gaba da jajircewa akan hakan. Mun yi shi a jamhuriyyar Nijar da Kano. Mun kafa ruhin ɗabi’a mai kyau da ingantaccen ilimi a tsakanin ɗalibanmu da ma’aikatanmu.

“Za mu tabbatar da inganci, tarbiyya, da kuma da’a a tsakanin dalibai da ma’aikatan Jami’ar Franco-British International University kamar yadda muke yi a Kano da Nijar,” in ji Farfesa Gwarzo.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
An Samu Ƙaruwar Garkuwa Da Mutane A Nijeriya – Rahoto

An Samu Ƙaruwar Garkuwa Da Mutane A Nijeriya - Rahoto

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version