Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar Noun Na Daukar Dalibai Kowane Lokaci A Bauchi – Farfesa Muhammad

by
4 years ago
in LABARAI
2 min read
Amurka Ta Ce Ba Za Ta Yarda Rasha Ta Yiwa Jami’anta Tambayoyi Ba
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Jami’ar karatu daga nesa ta kasa wato Open Unibersity reshen Bauchi ta ja hankalin matasa da ma’aikata su himmatu wajen shiga jami’ar don yin nazari kan fannoni dabam dabam da suke bukata a duk lokacin da suke so ko suka samu dama domin samun takardun shaidar ilmin jami’a masu inganci kamar yadda ake samu daga kowace irin jami’a da ake da ita a kasar nan.

Farfesa Mohammed Abdullahi Bello shugaban jami’ar karatu daga nesa NOUN ya bayyana cikin hirar sad a wakilin mu a ofishin sa da ke Bauchi, inda ya kara da cewa wannan jami’a ta Open Unibersity tana kara inganta ayyukan ta wajen ganin kowane mutum ya samu shiga ya karanta darasin da ya ke so a lokacin da ya ke bukata. Saboda suna daukar ma’aikatan gwamnati da ke son karatu a kowane lokaci da kuma samarin da suka rasa guraba a sauran jami’o’in da ake karatu a ciki saboda yadda dalibai ke bukatar guraba. Don haka kowane mutum zai iya shiga Open Unibersity ba tare da yayi jarrabawar JAMB ba, kuma zai iya shiga a kowane lokaci yake bukata ya kuma kammala a lokacin da ya ke so.

Ya kara da cewa basu da lokacin daukar dalibai ko lokacin kammalawa sai lokacin da mutum ya ke son ya shiga sai ya sayi takardar cikewa ya cika ta yanar gizo da takardun karatun sa, musamman wadanda ke da ilmin Difloma ko wadanda suka jima suna aikin gwamnati amma suna son yin digiri ko babban digiri ko digirin digirgir. Don haka ya bayyana cewa a Bauchi suna da dalibai sama da dubu biyar amma a kudancin Nijeriya kamar Jihar Lagos da sauran Jihohi ana samun dalibai dubu 20 zuwa 30 a jiha daya tak, kuma suna karatu suna kammalawa a duk lokacin da suke bukata shi ne banbanci da sauran jami’o’i da ke karatu cikin shekaru uku ko hudu su kammala.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Sauyin Sheka Yasa Majalisar Dokokin Kano Ta Dage Zamanta Na Ranar Litinin

Deborah: Kungiyar Gwamnonin Arewa Ta Bukaci A Zauna Lafiya

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

FOMWAN Da Meda Za Su Tallafi ’Yan Mata 50 Masu Talle A Garin Soro

Next Post

Kashi 95 Na ’Yan Kasuwar Filato Ke Neman Gwamnati Ta Ba Su Jari –Dafan

Labarai Masu Nasaba

Zargin Sauyin Sheka Yasa Majalisar Dokokin Kano Ta Dage Zamanta Na Ranar Litinin

Zargin Sauyin Sheka Yasa Majalisar Dokokin Kano Ta Dage Zamanta Na Ranar Litinin

by
13 hours ago
0

...

Deborah: Kungiyar Gwamnonin Arewa Ta Bukaci A Zauna Lafiya

Deborah: Kungiyar Gwamnonin Arewa Ta Bukaci A Zauna Lafiya

by
16 hours ago
0

...

Ganduje Ya Umurci Bala Ya Kula Da Ofishin Shugaban Ma’aikata Fadar Gwamnatin Kano

Ganduje Ya Umurci Bala Ya Kula Da Ofishin Shugaban Ma’aikata Fadar Gwamnatin Kano

by
20 hours ago
0

...

Deborah: Matasan Musulmai Ba Su Kona Min Gidana Ba —Bishop Kukah

Deborah: Matasan Musulmai Ba Su Kona Min Gidana Ba —Bishop Kukah

by Abubakar Abba
23 hours ago
0

...

Next Post

Kashi 95 Na ’Yan Kasuwar Filato Ke Neman Gwamnati Ta Ba Su Jari –Dafan

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: