CRI Hausa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home DAGA BIRNIN SIN

Jami’in Xinjiang: Amurka Wata Kasa Ce Da Ta Yi Kisan Kare Dangi

by CRI Hausa
January 13, 2021
in DAGA BIRNIN SIN
2 min read
Jami’in Xinjiang: Amurka Wata Kasa Ce Da Ta Yi Kisan Kare Dangi
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

A yayin taron manema labaru karo na 2 da aka shirya a nan Beijing, dangane da batun jihar Xinjiang ta kasar Sin a kwanan baya, wani jami’in jihar ya musunta karyar da masu adawa da kasar Sin da ke ketare suka yi, cewa wai ana sa ido kan mutane a jihar ta Xinjiang, tare da tilasta wa mutane yin aiki, har ma wai an yi kisan kare dangi a jihar.
A yayin taron, mataimakin darektar sashen kula da yayata jihar Xinjiang mai cin gashin kanta ta kasar Sin na kwamitin jihar na JKS Xu Guixiang, ya musunta karyar bisa hakikanin abubuwa da alkaluma, tare da yin karin bayani kan abubuwan da kasar Amurka ta yi, wajen keta hakkin dan Adam bisa tarihi, da ma halin da take ciki a yanzu.
Xu ya ruwaito alkaluman kididdiga dake cewa, yawan ‘yan kabilar Uyghur a Xinjiang ta karu daga mutum 10,171,500 a shekarar 2010 zuwa 12,718,400 a shekarar 2018, adadin da ya karu da kaso 25.04, yayin da yawan ‘yan kabilar Han ya karu daga 8,829,900 zuwa 9,006,800, adadin da ya karu da kaso 2 bisa dari. Ya ce azahiri take cewa, karuwar yawan ‘yan kabilar Uyghur ya fi karuwar al’ummar jihar baki daya, da karuwar ‘yan kananan kabilu, da ma karuwar ‘yan kabilar Han.
Haka zalika kuma, Xu ya nuna cewa, a daya hannu ana cin zalin al’ummu marasa rinjaye a kasar ta Amurka, wadanda aka dade ana nuna musu bambanci bisa tsari a fannonin siyasa, tattalin arziki, al’adu, da sauran sassan zaman al’ummar kasa.
Ya ce mutuwar George Floyd, wani Ba’amurke dan asalin Afirka a bara, da zanga-zangar da ta biyo bayan mutuwarsa, sun sake nuna yadda aka dade ana fama da wariyar launin fata bisa tsari a Amurka, lamarin da ya sanya al’ummu marasa rinjaye su kasa yin numfashi. (Tasallah Yuan)

SendShareTweetShare
Previous Post

Korona: Ba Ja Baya Ga Bude Makarantu – Gwamnatin Bauchi

Next Post

Sin Za Ta Kaddamar Da Shirin Samar Da Masu Tsaron Dazuka A Fadin Kasar

RelatedPosts

Allurar Rigakafin Da Sin Ta Samar Na Da Inganci

Allurar Rigakafin Da Sin Ta Samar Na Da Inganci

by CRI Hausa
4 hours ago
0

Ran 30 ga watan Disamba na shekarar bara, bayan allurar...

Rikicin Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Ya Jawo Asarar Guraben Ayyuka 245,000 A Amurka

Rikicin Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Ya Jawo Asarar Guraben Ayyuka 245,000 A Amurka

by CRI Hausa
9 hours ago
0

Wani nazari da cibiyar binciken harkokin tattalin arziki ta Oxford...

Amurka Za Ta Yi Wa Kanta Illa, Idan Ta Ci Gaba Da Hana Hajojin Jihar Xinjiang Shiga Kasar

Amurka Za Ta Yi Wa Kanta Illa, Idan Ta Ci Gaba Da Hana Hajojin Jihar Xinjiang Shiga Kasar

by CRI Hausa
9 hours ago
0

kwanan nan, hukumar kwastan da hukumar kare iyakokin Amurka, sun...

Next Post
Sin Za Ta Kaddamar Da Shirin Samar Da Masu Tsaron Dazuka A Fadin Kasar

Sin Za Ta Kaddamar Da Shirin Samar Da Masu Tsaron Dazuka A Fadin Kasar

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version