Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyar Matan Arewa Ta Yi Tir Da Kalaman Batanci

by
3 years ago
in LABARAI
2 min read
Jam’iyyar Matan Arewa Ta Yi Tir Da Kalaman Batanci
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Arewa Masu Kai Abinci Yankin Inyamurai Su Dakatar Saboda Kisa –Matasan Arewa A Kudu

EFCC Ta Bankado Gidaje 17 A Nijeriya Da Kasashen Waje Na Akanta Janar

Hajiya Ummi Tanko Yakasai, ita ce shugabar jam’iyyar Matan Arewa ta shaida wa manema labarai a Kano cewa jam’iyyar matan arewa ba ta goyon bayan kalaman batanci da wasu ‘yan siyasar kasar nan ke yi a kafafen yada labarai na kasar nan ganin ana shirye shiryen tunkaran zabukan 2019.
Jam’iyyar matan arewa zaman lafiya da aikata alhairi take goyon baya a fadin kasar nan. Sannan kuma ‘yan siyasa su fadin alhairi musamman a lokutan yakin neman zabe ba kalaman da za su karo rabuwar al’umma ba.
Malama Ummi Tanko Yakasai ta kara da cewa a matsayin su na iyaye mata, za su ci gaba da yin addu’oin fatan alhairi domin ganin a gudanar da zaben na 2019 lafiya. Duk kuma wanda Allah ya ba shi nasara a kan matsayin da yake nema ya tabbatar ya taimaka wa rayuwar mata da matasan kasar nan.
Alkawuran da yan siyasa suke yi wa al’umma su tabbatar sun cika masu musamman idan suka samu nasaran cin zabe idan kuma suka ki Allah zai tambaye su ranar gobe kiyama.
Da take tsokaci game da rayuwar matasan kasar nan Malama Ummi Tanko, ta ce kasar nan ba za ta ci gaba ba sai da rayuwar matasa nagari wanda al’uma za su yi alfahari da su. Sai da ta koka game da yadda wasu marasa kishin al’umma ke bai wa matasa kwayoyi masu sanya maye wanda suke tayar da hankula musamman a lokacin kamfen sai ta yi kira ga hukumomi da su kara himma wajen kawo karshen wannan dabi’u marasa kyau, su tabbatar sun tsare mutuncin matasa.
Matan da suka fito neman matsayi a cikin jam’iyyun kasar nan kuwa ta yi kira ga matan kasar nan su tabbatar sun kada masu kuri’un su ako wace jam’iyya suka fito, lokaci ya yi a cewar da za a gwada mata domin aga rawar da za su taka.
Daga karshe ta jawo hankulan duk wadanda Allah ya ba su matsayi tun daga kan shugaban kasa, gwamna da sanata da yan majilisar wakilai da sauran su da su tabbatar da shugabanci tsakani ga Allah ba tare da nuna banbanci ba domin yanzu abin da ake bukata a kasar nan shi ne hadin kai da fahimtar juna amma ta na zaton shugaban nin da za’a zaba za su yi adalci ga mata da maza da kuma al’umma gaba daya.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

PDP Na Kara Karbuwa A Jihar Kano

Next Post

Gaskiya Matakin Nasara: Nazari Daga Rayuwar Injiniya Suraj Yazid Abukur

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Arewa Masu Kai Abinci Yankin Inyamurai Su Dakatar Saboda Kisa –Matasan Arewa A Kudu

‘Yan Arewa Masu Kai Abinci Yankin Inyamurai Su Dakatar Saboda Kisa –Matasan Arewa A Kudu

by
5 hours ago
0

...

EFCC Ta Bankado Gidaje 17 A Nijeriya Da Kasashen Waje Na Akanta Janar

EFCC Ta Bankado Gidaje 17 A Nijeriya Da Kasashen Waje Na Akanta Janar

by
17 hours ago
0

...

Ana Kokarin Siffanta Kungiyar Dattawan Arewa A Matsayin Mai Zuga ‘Yan Tawaye A Nijeriya – Dr. Hakeem

Ana Kokarin Siffanta Kungiyar Dattawan Arewa A Matsayin Mai Zuga ‘Yan Tawaye A Nijeriya – Dr. Hakeem

by Abdulrazaq Yahuza Jere
1 day ago
0

...

Masarautar Zazzau Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Jama’atu Na Kai Karar Sarkinta

Masarautar Zazzau Ta Mayar Da Martani Kan Zargin Jama’atu Na Kai Karar Sarkinta

by Abubakar Abba
2 days ago
0

...

Next Post
Gaskiya Matakin Nasara: Nazari Daga Rayuwar Injiniya Suraj Yazid Abukur

Gaskiya Matakin Nasara: Nazari Daga Rayuwar Injiniya Suraj Yazid Abukur

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: