Jam'iyyun Hamayya Ku Zo Mu Haɗa Kai, Mu Gina Jihar Adamawa - Fintiri 
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jam’iyyun Hamayya Ku Zo Mu Haɗa Kai, Mu Gina Jihar Adamawa – Fintiri 

byMuh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
Adamawa

Gwamna Ahmadu Umaru Fintiri, ya jaddada bukatar samun hadinkan jama’a da bangarorin jam’iyyu da ‘yan siyasar jihar domin bashi damar samun gina jihar Adamawa.

Fintiri, ya bayyana haka ne a wani taron gagarumin tarban da jama’a magoya baya suka shirya masa ranar Juma’a, lokacin da ya dawo Yola fadar jihar tun bayan da kotun Koli ta ayyanashi a matsayin halastaccen gwamna.

  • Hukuncin Zaben Adamawa: Na Rungumi Kaddara – BinanBinani
  • Kotun Koli Za Ta Saurari Shari’ar Zaben Gwamnan Adamawa A Ranar Litinin 

Gwamna Umaru Fintiri, ya ci gaba da cewa “gwamnatina ba zata bada damar gudanar da wargi da hayaniya ko hamayya irin na siyasa marar ma’ana ba, kuma ba zai yi kasa a gwiwa ba wajen ganin an samar da tsarin dimokuradiyya ga kowane dan jihar.

“A ko da yaushe gwamnatina na kan gaba wajen tafiyar da al’umma, ba tare da la’akari da matsayar da suke kanta ko jam’iyyarsu ba, ina kira ga ‘yan jiha da su bamu goyon baya don gina jihar da suke so da kuma burin ganin ta ci gaba.

“Ba mu taba haifar cece-koce ko wani gibi a shugabanci ba, a ko da yaushe muna tabbatar wa al’ummar jiha cewa za mu yi musu aiki, da kuma yi musu abinda ya kamata, ba mu taba shagaltuwa ko na dakika guda ko domin hayaniyar ’yan siyasa kan da nauyin dake kanmu ba” inji Fintiri.

Da yake magana kan hukuncin kotun koli kuwa, gwamnan ya yabawa bangaren shari’ar, ya kara da cewa “hukuncin kotun ya zaburar dani wajen kara gwazo, zanyi iyakacin kokarina da tsayawa tsayin daka da kuma tabbatar da cewa an yi adalci ga jama’a.

“Ban taba rasa imani da bangaren shari’a ba, na fadi lokacin babu adadi, sun tsaya tsayin daka su na gudanar da aikinsu yadda ya dace, hukunce-hukuncensu bai kasance cikin rudani kamar yadda Hudu Ari ya yi wa hukumar zabe INEC ba.

“Don haka zan ci gaba da hadakai da bangaren shari’a domin mu gina dimokuradiyya da gina jiha da kasarmu” inji Fintiri.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Sojoji

Sojoji A Jihar Katsina Sun Fatattaki ‘Yan Bindiga Tare Da Kubutar Da Mutane

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version