Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Jerin Manyan Kusoshi A Nijeriya Da Suka Kamu Da Cutar Kwarona

by
2 years ago
in Uncategorized
4 min read
Daga 25 Ga Rajab Zuwa … Ga Sha’aban 1441, Bayan Hijira
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Tun bayan da aka samu wasu a Nijeriya da ke dauke da Cutar Kwarrona (Cobid-19) inda daga ranar 27 ga watan Fabrairun wannan shekara, a kullu yaumin ana kara samun yawaitar masu kamuwa da cutar.

A ranar 7 ga watan Afrilu da misalign karfe 09:30 na dare, an samu tabbacin mutane 254 wadanda ke dauke da wannan cuta ta Cobid-19 a Nijeriya daga Cibiyar kula tare da hana yaduwar cutuka ta kasa (NCDC). Inda aka kuma bayar da tabbacin mutuwar mutane 7 tare da sallamar kimanin 44 bayan sun warke daga wannan cuta.

Kazalika, mafi yawancin wadanda aka samu da wannan cuta, mutane wadanda a kusa-kusan nan ke da tarihin tafiye-tafiye zuwa kasashen waje ko kuma yin mu’amala da su. A cikin wadannan manyan mutane ko masu rike da madafun iko a Nijeriya akwai wadanda suka warke bayan sun jima suna fama da ita, a karshe kuma aka tabbatar da cewa ba sa dauke da wannan cuta Cobid-19.

Labarai Masu Nasaba

Dakarun MNJTF Sun Yi Barin Wuta Kan ‘Yan Boko Haram Sun Kashe 300 A Tafkin Chadi

CAN Ta Shirya Zanga-Zangar Yin Allah Wadai Da Kisan Deborah A Duk Jihohin Nijeriya

Ga dai jerin wadannan manyan kusoshi a Nijeriya wadanda suka kamu da wannan cuta, lokaci bayan lokaci bayan yi musu gwaji aka kuma same su da ita.

  1. Abba Kyari

A ranar 24 ga watan Mayun wannan shekara ne aka sanar da cewa, Babban Shugaban Ma’aikatan Gidan Gwamnatin Tarayya, ya kamu da wannan cuta ta Cobid-19. Bisa dukkanin alamu kuma, ya kamu da cutar ne a yayin da ya yi tafiya Kasar Germany da kuma Egypt. Inda daga bisani a ranar 29 ga watan Mayu, aka garzaya da shi zuwa Jihar Legas domin yi masa magani.

  1. Nasir El-Rufai

Gwamnan Jihar Kaduna, shi da kansa ya bayyana a shafinsa na twitter cewa, an yi masa gwaji, an kuma tabbatar da cewa yana dauke da wannan cuta ta Cobid-19. Sannan, a halin yanzu yana nan yana samun kulawa ta hanyar shan magani.

  1. Bala Mohammed

Shi ma Gwamnan Jihar Bauchi, an bayar da sanarwar yana dauke da wannan cuta a ranar 24 ga watan Mayu, bayan an yi masa gwaji. Kamar yadda rahotannin suka bayyana, Gwamnan ya dawo Jihar Bauchi daga Legas, inda ya hadu da dan tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Alhaji Atiku Abubakar a jirgi, wanda shi ma aka same shi dauke da wannan cuta. Kamar yadda dai rahoton ya bayyana, sun yi musabiha da juna tare da tattaunawa a tsakaninsu a cikin wannan jirgi da suka hau tare, inda ake kyautata zaton a wannan haduwa ne Gwamnan ya kamu da wannan cuta.

  1. Seyi Makinde (ya warke)

Haka nan, Gwamnan Oyo, a ranar 30 ga watan Mayu aka tabbatar da tasa kamuwar daga wannan cuta. Kamar yadda aka bayyana a halin yanzu cewa, ya warke bayan sake yi masa wani gwajin a karo na biyu, amma duk da haka yana nan a kadaice.

  1. Mohammed Atiku Abubakar

Kamar yadda aka sani, Mohammed guda ne cikin ‘ya’yan tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Atiku Abubakar. Mahaifin nasa ne a ranar 22 ga watan Mayu, ya sanar da cewa, dan nasa na dauke da wannan cuta. Tun bayan wannan lokaci kuma, yana can a Abuja yana karbar magani yana kuma samun sauki kamar yadda ya bayyana da kansa.

 

  1. Chioma Rowland

Sannan Chioma, budurwar Mawakin nan mai suna Dabid Adeleke, wanda aka fi sani da Dabido, ita ma ta kamu da wannan cuta ta Cobid-19. Dabid din ne ya bayyana haka, a shafinsa na Instagram cewa budurwar tasa na dauke da wannan cuta, sannan shi da sauran mutanensa su 31 za su je a yi musu gwaji sakamakon tafiya da suka yi zuwa Kasar Amurka.

  1. Farfesa Jesse Otegbayo (ya warke)

Shugaban Asibitin Koyarwa na Jami’ar Kwalejin (UCH) Ibadan, Farfesa Jesse Otegbayo, shi ma an tabbatar day a kamu da wannan cuta ta hanyar yin gwaji a ranar 29 ga watan Mayu. Wanda shi ma tuni aka bayyana cewa, ya warke ta hanyar sake yi masa gwaji a karo na biyu.

  1. Muhammed Babandede

Muhammed Babandede, Shugaban Hukumar Shige da Fice ta Kasa, kamar yadda ya bayyana da kansa, ya killace kansa tun bayan dawowarsa daga Kasar Ingila a ranar 22 ga watan Mayun wannan shekara, inda ya zargi kansa da kamuwa da wannan cuta.

  1. Farfesa Ezekiel Olapade-Olaopa

Shugaban Jami’a na Kwalejin Lafiya, Farfesa Ezekiel, shi ma ya kamu da wannan cuta ta Cobid-19, bayan yi masa gwaji. Kamar yadda rahotanni suka nuna kuma, a halin yanzu babu wasu alamu da ke nuna cewa yana dauke da wannan cuta, duk da cewa yana cigaba da karbar magani.

  1. Farfesa Obafunke Denloye

Farfesa Obafunke, Shugaban Kwalejin Lafiya na Jami’ar Ibadan, shi ma na cikin guda daga cikin manyan kusoshin wannan kasa, wadanda suka kamu da wannan cuta ta Koronabairus a Nijeriya.

 

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Hanyar Kaduna Zuwa Jos Ta Zama Tarkon Mutuwa – Ado Ibrahim Kaku

Next Post

Yadda Masu Kamuwa Da Cutar Kwarona Ke Warkewa A Nijeriya – NCDC

Labarai Masu Nasaba

An Yi Lugudan Wuta Ta Jiragen Yaki Kan Isis An Kashe Kwamandanta Bin-umar A Tabkin Chadi

Dakarun MNJTF Sun Yi Barin Wuta Kan ‘Yan Boko Haram Sun Kashe 300 A Tafkin Chadi

by Leadership Hausa
21 hours ago
0

...

CAN Ta Shirya Zanga-Zangar Yin Allah Wadai Da Kisan Deborah A Duk Jihohin Nijeriya

CAN Ta Shirya Zanga-Zangar Yin Allah Wadai Da Kisan Deborah A Duk Jihohin Nijeriya

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

...

Ramadan: Diyar Marigayi Sheikh Ja’afar Ta Fara Tafsirin Al-qur’ani A Masallacinsa Da Ke Kano

An Kashe Mutum 172, An Yi Garkuwa Da 23 A Arewa Maso Gabashin Nijeriya Cikin Watanni 3 —Rahoto

by Leadership Hausa
6 days ago
0

...

2023: Shekarau, Barau Da Kawu Sumaila Na Shirin Ficewa Daga APC zuwa NNPP Kwankwasiyya

2023: Shekarau, Barau Da Kawu Sumaila Na Shirin Ficewa Daga APC zuwa NNPP Kwankwasiyya

by
1 week ago
0

...

Next Post
NCDC Ta  kaddamar da Sabon Ofishi A Kebbi

Yadda Masu Kamuwa Da Cutar Kwarona Ke Warkewa A Nijeriya - NCDC

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
 

Loading Comments...
 

    %d bloggers like this: