CRI Hausa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home DAGA BIRNIN SIN

Jerin ’Yan JKS Da Amurka Ta Fidda Babbar Karyar Ce Don Bata Sunan Kasar Sin

by CRI Hausa
December 16, 2020
in DAGA BIRNIN SIN
2 min read
Jerin ’Yan JKS Da Amurka Ta Fidda Babbar Karyar Ce Don Bata Sunan Kasar Sin
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Kwanan baya, kafofin watsa labaran wasu kasashen yammacin duniya kamar Burtaniya da Australia da sauransu, sun ce, wani bayanin dake kunshe da sunayen wasu ‘yan jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin wato JKS guda miliyan 1.95 na nuna cewa, ‘yan JKS suna aikin leken asiri a wasu hukumomi da kamfanonin yammacin kasashen duniya dake kasar Sin. A sa’i daya kuma, sun ce, ba su da shaidun dake gaskata wannan zargin da suka yi.

To, idan basu da shaidu, me ya sa, suka yar da da irin wannan labari game da kasar Sin?
Ko shakka babu, suna neman bata sunan kasar Sin ne kawai, domin nuna kiyayya.
Idan muka duba asalin wannan labari, za a gane gaskiyar hakan.
Da farko, kafofin watsa labaran kasashen sun ce sun sami bayani daga kungiyar hadin gwiwar nazarin manufofi kan kasar Sin wato IPAC, wadda aka kafa a watan Yuni na bana, bisa jagorancin dan majalisar dokokin kasar Amurka Marco Rubio. Gaba daya akwai mambobi guda 18 da suka zo daga kasashe 8 cikin wannan kungiya, wadanda su kan yada jita-jita game da harkokin kasar Sin dake shafar yankin Hong Kong, da jihar Xinjiang da kuma jihar Tibet da sauransu.
Kana, kwanan baya, gwamnatin kasar Sin ta kakaba wa Marco Rubio takunkumin, bisa yadda yake tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasar Sin. Shi ya sa, ya fitar da wannan jerin ‘yan JKS domin mayar da martani, wanda hakan ya kasance wata karya da ya tsara domin bata ran al’ummomin Sin.
Sa’an nan kuma, idan mun duba bayanin da kungiyar ta fidda, cewar, sabo da akwai ‘yan JKS dake aiki cikin wadannan kamfanoni da hukumomin kasashen ketare dake kasar Sin, shi ya sa, ake ganin cewa, kasar Sin tana leken asirin kasashen. Lalle sun yi wannan zato ne domin rashin sani game da kasar Sin, ko kuma kawai, suna neman bata sunan kasar ta Sin ne bisa wannan hujja maras tushe.
A hakika dai, gaba daya akwai ‘yan JKS kimanin miliyan 92 a kasar Sin, wadanda suke aiki a sana’oi iri daban daban, shi ya sa, ba abin mamaki ba ne, ace akwai ‘yan JKS dake aiki cikin hukumomi ko kamfanonin ketare dake kasar Sin. Suna gudanar da ayyukansu yadda ya kamata, sun kuma samu amincewa daga kamfanoninsu. Haka kuma, wadannan kafofin yada labaran yammacin duniya sun ce, a halin yanzu, babu shaidun dake nuna cewa, akwai ‘yan JKS dake gudanar da aikin leken asiri. Lalle ba su da hankali.
Bisa wadannan dalilai, gaskiyar lamarin shi ne, wannan babbar karya ce da masu adawa da kasar Sin na yammacin kasashen duniya suka tsara, domin bata sunan kasar Sin. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Zulum Ya Gana Da ‘Yan Gudun Hijirar Borno A Chadi

Next Post

Sin Ta Bayar Da Tallafin Kayayyakin Kiwon Lafiya Ga Asibiti Mafi Girma A Zimbabwe

RelatedPosts

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Duba Marasa Lafiya Sama Da 4,000 A Ghana A 2020

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Duba Marasa Lafiya Sama Da 4,000 A Ghana A 2020

by CRI Hausa
1 day ago
0

Tawagar jami’an lafiya ta kasar Sin kashi na 9 dake...

Amurka Ta Kasa Magance Matsalar Rashin Daidaito A Cikin Al’ummarta

Amurka Ta Kasa Magance Matsalar Rashin Daidaito A Cikin Al’ummarta

by CRI Hausa
1 day ago
0

Sakamakon bazuwar cutar COVID-19, wadda ta raunana tattalin arzikin duniya...

Mike Pompeo Zai Kammala Aikinsa Na Ministan Harkokin Waje

Mike Pompeo Zai Kammala Aikinsa Na Ministan Harkokin Waje

by CRI Hausa
1 day ago
0

A cikin kwanaki 10 da wani abu da suka gabata,...

Next Post
Sin Ta Bayar Da Tallafin Kayayyakin Kiwon Lafiya Ga Asibiti Mafi Girma A Zimbabwe

Sin Ta Bayar Da Tallafin Kayayyakin Kiwon Lafiya Ga Asibiti Mafi Girma A Zimbabwe

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version