Jihar Zamfara Ce Kan Gaba Wajen Tattara Kuɗaɗen Shiga A Shekarar 2024 - Rahoto
  • English
  • Business News
Tuesday, October 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihar Zamfara Ce Kan Gaba Wajen Tattara Kuɗaɗen Shiga A Shekarar 2024 – Rahoto

byLeadership Hausa and Sulaiman
11 months ago
Zamfara

An sanya Jihar Zamfara a matsayin jihar da ke kan gaba a cikin Ayyukan Tattara Kuɗaɗen Shiga na Cikin Gida a Nijeriya (IGR).

 

A wani rahoton wata ƙungiya mai bibiyar harkokin kasafin kuɗi da ake kira BudgIT na 2024, wanda aka ƙaddamar a makon da ya gabata a ranar Talata, bugu ne na shekara-shekara da ke kimanta ayyukan kasafin kuɗin kowace jiha na dogon lokaci da kuma ɗorewar kasafin kuɗin.

  • Kotu Ta Soke Tuhumar Da Ake Yi Wa Yaran Da Aka Kama Yayin Zanga-zangar Yinwa
  • Ƙungiyar Likitoci Ta Buƙaci Dakatar Da Kwamishina Kan Zargin Cin Zarafin Likita A Kano

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa babban ci gaban da aka samu wajen bunƙasar kuɗaɗen shiga na jihar Zamfara da kashi 240.44% na da nasaba da matakin da jihar ta ɗauka na cewa ba wai kawai ta dogara ne kocokan kan kason kuɗin da take samu daga ga Gwamnatin Tarayya (FAAC) ba ne.

Zamfara
Sakamakon rahoton kungiyar

Sanarwar ta ƙara da cewa, rahoton na BudgIT ya samu ne ta hanyar nazari da tantancewa da kuma ƙididdigar ayyukan kasafin kuɗi na dukkan jihohi 36, daga mafi yawa zuwa mafi ƙaranci.

 

Rahoton na BudgIT ya bayyana gagarumin ci gaban da ake samu a jihar Zamfara ta hanyar tattara kuɗaɗen shiga na cikin gida (IGR), inda ya nuna cewa daga jiha ta 36 a shekarar 2023, Zamfara ta kai matsayi na 26 a shekarar 2024.

 

“Wannan gagarumin aikin za a iya danganta shi da yunƙurowar jihar bayan da ta samu koma baya na kashi 49.75 cikin 100 na IGR na shekarar 2022, inda ta ƙara da kashi 240.22% daga biliyan N6.51 a shekarar 2022 zuwa biliyan N22.16 a shekarar 2023.

 

“Ana samun ci gaban sosai a bangaren IGR na Zamfara duk shekara: Harajin ta na shiga ya ƙaru da kashi 142.26% daga biliyan N5.03 a 2022 zuwa biliyan N12.18, lasisi ya ƙaru da 5921.22% daga miliyan N22.78 a 2022 zuwa N1.37 Biliyan a 2023, Kuɗaɗen sun ƙaru da kashi 3610.38% daga miliyan N82.44 a 2022 zuwa biliyan N3.06 a 2023.

 

“Bugu da ƙari, tarar ta tashi da kashi 1924.52% daga miliyan N24.15 a 2022 zuwa miliyan N491.32 a 2023, ayyukan tallace-tallace ya ƙaru da kashi 32.49% daga miliyan N772.06 a 2022 zuwa biliyan N1.02 a 2023, abin da ake samu ya ƙaru da kashi 5.7% zuwa 582% a 2022 zuwa miliyan N562.48 a 2023, kuma abin da ake samu daga sauran haraji ya ƙaru da kashi 519.71% daga miliyan N412.03 a 2022 zuwa biliyan N2.55 a 2023.

 

“Bugu da ƙari kuma, jihar ta samu kuɗaɗen shiga daga hayar gine-ginen gwamnati, hayar filaye da sauran su da samun kaɗaɗe daga zuba hannun jari duk an shigar da su cikin kuɗaɗen shiga a shekarar da ta gabata. Zamfara za ta iya nuna aniyar inganta tattalin arzikinta ta hanyar binciko albarkatun ƙasa tare da haɗin gwiwar Gwamnatin Tarayya don karkato da hanyoyin samun kuɗaɗen shiga.

 

“Jimillar kuɗaɗen shigar jihar ya ƙaru da kashi 65.35% zuwa Naira Biliyan 144.95 a shekarar 2023 daga Naira Biliyan 87.68 da ta samu a shekarar da ta gabata. Dangane da tsarin kuɗaɗen shigar da ake samu akai-akai, alamun masu ƙarfi sun nuna cewa jihar na fuskantar raguwar samun kuɗaɗen shiga daga shekarar da ta gabata yayin da dogaro kacokan kan kason kuɗin da take samu daga Gwamnatin Tarayya daga kashi 90.52% a shekarar 2022 zuwa kashi 74.66% a shekarar 2023, duk da rabon kuɗin da kashi 4.93% daga biliyan N62.21 zuwa biliyan N65.28. A ƙarshe, Ayyukan Tattara Kuɗaɗen Shiga na Cikin Gida a Nijeriya (IGR) zuwa rabon kuɗaɗen shiga na yau da kullum na 2023 ya kasance kashi 22.16% sama da kashi 9.48% a cikin 2022.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci
Labarai

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Next Post
Xi Ya Bukaci A Gina Rundunar Sojin Sama Mai Karfi Kuma Na Zamani

Xi Ya Bukaci A Gina Rundunar Sojin Sama Mai Karfi Kuma Na Zamani

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Na Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Korea Ta Arewa

Firaministan Sin Zai Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Na Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Korea Ta Arewa

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version