Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home MANYAN LABARAI

Ka Sake Ba Ni Beli – Maina Ga Alkali

by Muhammad
January 21, 2021
in MANYAN LABARAI
2 min read
Maina
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
  • Ya Ce, Da Gaske Ba Shi Da Lafiya

Daga Khalid Idris Doya,

Tsohon shugaban kwamitin farfado da tara kudaden fansho na kasa (PRTT), Abdulrasheed Maina, a jiya Laraba, ya sake rokon Alkalin babban kotun tarayya da ke Abuja, Justice Okon Abang, da ya bayar da belinsa.

Maina, a wata bukatar da ya gabatar mai kwanan wata 24 ga Disamba, 2020, da ke dauke da lamba kamar haka: FHC/ABJ/CR/258/19 ta hannun lauyansa, Anayo Adibe, ya shaida cewar, bukatar hakan ya zama dole ne lura da halin rashin lafiya da ke damunsa, wacce har batun ya kai ga tsananta.

Amma kotun ba ta zauna ba, domin sauraron wannan bukatar ba, inda ta dage shari’ar zuwa wani rana.

Kotun dai ta dage cigaba da sauraron shari’ar har zuwa 1 ga Fabrairun da ke tafe.

Shi dai Maina idan za ku iya tunawa a shekarar da ta gabata kotun ta taba bada belinsa kan miliyan 500 tare da gabatar da Sanatan da ke wakiltar Borno ta kudu, Ali Ndume a matsayin wanda ya tsaya masa wajen amsar belinsa.

Justice Abang, bayan jerin zaman da kotun ta yi ba tare da ganin Maina ba, ya sanya Alkalin soke izinin belin Maina din da ya bayar, tare da bada umarni mai karfi ga jami’an tsaro da su kamo shi a duk inda suka yi tozani da shi.

Lamarin da har ya kai ga kotun daure Sanata Ndume na ‘yan kwanaki sakamakon kaza kawo wanda ya tsaya masa a gaban kotu, kodayake daga baya kotun ta bada belin Ndume bisa nuna halin kwarai da biyayya da ya nuna, inda kotun ta ci gaba da shari’arta duk da babu Maina har zuwa lokacin da aka sake kamo shi gami da tuso kesarsa zuwa gaban kotun.

A dai ranar 4 ga watan Disamban 2020 ne EFCC ta sake kawo Maina gaban kotun bayan shafe wasu watanni da arce wa belinsa da aka bayar tun farko, domin cigaba da gurfanar da shi kan zarge-zargen da hukumar ke masa.

SendShareTweetShare
Previous Post

Fashewar Tankar Mai Ya Ci Rayuwar Mutum Uku Da Jittaka Shida A Ogun

Next Post

Gina Hanyar Ruwa: Babu Kudin Kowa A Cikin Wannan Babban Aiki, Inji Mai Turaka

RelatedPosts

Hijira

Zulum Ya Bankado ’Yan Hijira 650 Na Bogi

by Muhammad
24 hours ago
0

Ya Sake Koma Wa Dikwa Bayan Harin Boko Haram Daga...

Allurar Rigakafin

An Fara Yin Allurar Riga-kafin Korona a Nijeriya

by Muhammad
3 days ago
0

Yau Ake Sa Ran Buhari Da Osinbajo Za Su Karbi...

'Yan Adaidaita

An Sasanta Yajin Aikin ’Yan Adaidaita Bayan… Motocin ‘Kano Line’  Sun Koma Jigilar Jakara-Kasuwa

by Muhammad
2 weeks ago
0

Babu Hanunmu A Ciki Wannan Yaji – Shugaban ’Yan Adaidaita...

Next Post
Gina Hanyar Ruwa: Babu Kudin Kowa A Cikin Wannan Babban Aiki, Inji Mai Turaka

Gina Hanyar Ruwa: Babu Kudin Kowa A Cikin Wannan Babban Aiki, Inji Mai Turaka

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version