CRI Hausa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home DAGA BIRNIN SIN

Kafofin Watsa Labaran Birtaniya: Huawei Zai Kai Bankin HSBC Kara Domin Samun Muhimman Takardun Bankin

by CRI Hausa
February 13, 2021
in DAGA BIRNIN SIN
2 min read
Kafofin Watsa Labaran Birtaniya: Huawei Zai Kai Bankin HSBC Kara Domin Samun Muhimman Takardun Bankin
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Rahotannin da kamfanin BBC da jaridar The Guardian na kasar Birtaniya suka bayar sun nuna cewa, a ranar 12 ga wata, agogon kasar, lauyan babbar jami’ar kudi ta kamfanin Huawei na kasar Sin Meng Wanzhou zai gabatar da kara ga babbar kotun birnin London domin samun muhimman takardun bankin HSBC.

Kamfanin Huawei ya dauki matakin ne domin shaida cewa, karar da kasar Amurka ta kai madam Meng Wanzhou kan boyewa bankin HSBC huldar dake tsakanin kamfanin Huawei da kamfanin fasaha na Skycom na yankin Hong Kong na kasar Sin, inda sanadiyyar hakan, bankin na Birtaniya ya ci gaba da hidimtawa Huawei, ba ta gaskiya ba ce.
Jaridar The Guardian ta ruwaito kalaman kamfanin Huawei cewa, kamfanin ya bukaci kotun London da ta ba da umurnin samar da bayanan da abin ya shafa, alal misali ma’aikatan bankin HSBC nawa ne suka san taron da aka kira a Hong Kong, da abubuwan da aka tattauna yayin taron, da adadin ma’aikatan bankin da suka san sakamakon taron, da sauransu.
A watan Yulin bara rahotannin manhajar watsa labarai ta jaridar The People’s Daily ta kasar Sin sun bayyana cewa, Amurka ta gabatar da “takardun karar da aka yi rajista” ga kotun kasar Canada, inda ta bayyana cewa, babbar jami’ar kudin kamfanin Huawei Meng Wanzhou ta boyewa bankin HSBC huldar dake tsakanin kamfaninta da kamfanin fasaha na Skycom na yankin Hong Kong na kasar Sin, inda bankin HSBC na Birtaniya ya ci gaba da samar da hidima ga Huawei, a sanadiyyar haka, bankin HSBC ya sabawa dokar takunkumin da Amurka ta sanyawa Iran, har ya gamu da matsalar aikata laifi, a don haka an yanke shawara cewa, Meng Wanzhou ta yaudari bankin HSBC.
Amma hakika kamfanin HSBC ya yi karya, ya san huldar dake tsakanin kamfanin Huawei da kamfanin Skycom na yankin Hong Kong, saboda an gano cewa, kamfanin Skycom na Hong Kong da kamfanin Huawei suna gudanar da hadin gwiwa a yankunan kasar Iran, shaidun mai kwari sun nuna cewa, bankin HSBC ya san harkokin kamfanin Huawei a Iran, kuma a shekarar 2010, sakwannin da aka tura tsakanin bangarori uku wato bankin HSBC da kamfanin Huawei da kuma kamfanin Skycom sun shaida cewa, bankin HSBC ya san huldar dake tsakanin Huawei da Skycom sosai, kana daga takardun harkokin kudin kamfanin Skycom tsakanin shekarar 2009 zuwa 2010 da kamfanin Huawei ya tura ga bankin HSBC, an lura cewa, bankin HSBC ya fahimci daukacin harkokin kamfanin Skycom na Hong Kong dake Iran.
Hakazalika, jaridar The Guardian ta ruwaito kalaman lauyan madam Meng Wanzhou cewa, an jirkita takardun manhajar PPT da ta gabatar wa bankin HSBC, domin ana son yada jita-jitar wai Meng Wanzhou ta boye huldar dake tsakanin kamfanin Huawei da kamfanin Skycom na Hong Kong.(Mai fassarawa: Jamila daga CRI Hausa)

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Domin Karfafa Tsaron Iyaka, NIS Ta Kaddamar Da Sansaninta Na Belel

Next Post

Matakin Sin Na Dakatar Da Kafar BBC Ya Hallata

RelatedPosts

Gwamnatin Biden Na Bin Hanyar Da Tsohuwar Gwamnati Ta Rage Mata Wajen Gudanar Da Harkokin Dake Da Nasaba Da Kasar Sin

Gwamnatin Biden Na Bin Hanyar Da Tsohuwar Gwamnati Ta Rage Mata Wajen Gudanar Da Harkokin Dake Da Nasaba Da Kasar Sin

by CRI Hausa
12 hours ago
0

Daga CRI Hausa Gwamnatin Biden ta cika wata guda da...

Karyar Da Kasashen Yamma Ke Kitsawa Game Da Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ba Ta Samu Shiga Ba

Karyar Da Kasashen Yamma Ke Kitsawa Game Da Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ba Ta Samu Shiga Ba

by CRI Hausa
12 hours ago
0

Daga CRI Hausa Shahararren marubucin litattafan nan dan kasar Faransa...

Kafar Watsa Labaran Amurka: Yadda JKS Ta Samu Amincewar Al’umma

Kafar Watsa Labaran Amurka: Yadda JKS Ta Samu Amincewar Al’umma

by CRI Hausa
12 hours ago
0

Daga CRI Hausa A gabannin cika shekaru 100 da kafa...

Next Post
Matakin Sin Na Dakatar Da Kafar BBC Ya Hallata

Matakin Sin Na Dakatar Da Kafar BBC Ya Hallata

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version