Kamala Harris Na Ci Gaba Da Samun Goyon Bayan Takara A Democrat
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamala Harris Na Ci Gaba Da Samun Goyon Bayan Takara A Democrat

byRabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Vice President Kamala Harris takes her official portrait Thursday, March 4, 2021, in the South Court Auditorium in the Eisenhower Executive Office Building at the White House. (Official White House Photo by Lawrence Jackson)

Vice President Kamala Harris takes her official portrait Thursday, March 4, 2021, in the South Court Auditorium in the Eisenhower Executive Office Building at the White House. (Official White House Photo by Lawrence Jackson)

Mataimakiyar Shugaban Amurka, Kamala Harris ta samu goyon baya mai rinjaye na wakilan jam’iyyar Democrat domin kasancewa ‘yar takarar shugabancin kasar a jam’iyyar.

Wani bincike da kamfanin dillancin labarai na Associated Press ya yi ya nuna cewa Kamala ta samu goyon baya daga wakilan jami’iyyar fiye da 1,976 da take bukata ta samu nasarar zama ‘yar takarar jam’iyyar a zagayen farko na zaben.

  • Za A Ci Gaba Da Daukar Shirin ‘The Mandate’ A Kasar Faransa – Ezinne Agwu
  • Kamfe: An Tara Wa Kamala Haris Kusan Dala Miliyan 50 Cikin Sa’o’i 2 A Amurka

Hakan kuwa na nufin Misis Harris na dab da zama ‘yar takarar shugabancin kasar ta jam’iyyar ta Democrat domin karawa da dan takarar jam’iyyar Republican, Donald Trump a babban zaben na watan Nuwamba.

Sai dai hakan zai zama a hukumance ne kawai lokacin da wakilan jam’iyyar da za su zaben suka kada kuri’a a babban taron jam’iyyar a Chikago a wata mai kamawa.

Wakilan dai su ne mutanen da ke wakiltar mazabunsu. Kuma alkawarin goyon bayan da suka sanar bai zama wajibi su bi ba har sai lokacin kada kuri’a duk da dai da wuya hakan ya sauya.

har yanzu dai babu wani da ya fito a bayyane ya kalubalanci Misis Harris tun bayan da shugaba Joe Biden ya sanar da ficewa daga takarar ranar Lahadi.

Ya fuskanci matsin lamba daga jiga-jigan jam’iyyar ta Democrat sakamakon rashin katabus a mahawarar da ya yi da Mista Trump.

Idan dai har irin goyon bayan da take samu zai zama kuri’a a lokacin taron jam’iyyar Democrat da za a yi tsakanin ranar 1 zuwa 7 ga watan Agustan 2024, to Misis Harris za ta zamo ‘yar takarar jam’iyyar.

Binciken na AP na nuni da irin girman goyon bayan da Kamala Harris ke samu tun bayan da Joe Biden ya sanar da ajiye takarar tasa.

Har wayau wani abu shi ne yadda aka tara wa Kamala Harris tallafin miliyoyin Daloli tun bayan sanarwar ficewar ta Mista Biden sanna kuma jiga-jigan jam’iyyar ta Democrat sun shirya goya mata baya.

Ana sa ran Misis Harris za ta bayyana a wani gangamin magoya baya a Milwaukee da ke Jihar Winsconsin ranar Talata kuma wanda shi ne zai zama gangaminta na farko tun bayan da Mista Biden ya fice daga takarar kuma ya goyi bayan mataimakiyar tasa.

A wani bangaren kuma Mista Biden zai koma fadar White House bayan kwashe dan wani lokaci sakamakon kamuwa da cutar Korona. Mista Biden zai gana da firaiministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu a wannan makon a yayin ziyarar da Netanyahun zai kai Washinton.

Da take jawabi ga ma’aikata a ofishin kamfe dinta a Wimington a Jihar Delaware Misis Harris alamu sun nuna ta shirya wa Mista Trump.

Da take bayyana kanta a matsayin mai shari’ar da ta hukunta masu laifi, sai ta kara da cewa: “Na san irin su Donald Trump.”

Ta kara da cewa takarar Biden da Harris ta zamo wani da ke alamta kishin makomar Amurka da tasu da kuma ta Donald Trump.

“Wani yana duba gaba, dayan kuma yana waiwayen baya,” Harris ta ce. “Donald Trump yana son komar da kasarmu baya mu kuma mun yi imani da makoma mai kyau da za ta yi kyau ga dukkannin Amurkawa.”

Ta kuma yi nuni da irin nasarorin da Mista Biden ya samu, tana mai cewa aikin da ta yi tare da shi a matsayinta na mataimakiyar shugaban kasa “shi ne wani abun da cimma babba a rayuwarta”.

kafin dai Misis Harris ta hau dandamalin kmafe ta fara magana, sai da mista Biden ya fara yin tsokaci ta wayar tarho a wani yanayi na farko tun bayan sanarwar da ya yi na ficewa daga takarar bayan kamuwa da cutar korona.

Ya fara ne da yin godiya ga masu taimaka masa inda ya nemi da su “rungumi” Misis Harris saboda “ita ce ta fi dacewa”.

“Na san cewa labarin da kuka ji jiya ya girgiza ku to sai dai abin da ya fi dacewa a yi kenan,” In ji Mista Biden.

Ya kuma sha lawashin shiga gangamin nema mata kuri’a kan-jiki-kankarfi kasancewar yadda mulkin demokradiyya ke fuskantar barazana.

Shi kuma mataimakin Donald Trumpna jam’iyyar Republican, Sanata JD Bance, ya soki Misis Harris da Mista Biden baki dayansu a lokacin yakin neman zabe a Birginia.

“Tarihi zai rinka tuna wa da Joe Biden ba kawai a matsayin dan takarar da ya gudu ya bar ladansa ba, har ma da kasancewarsa shugaban Amurka da ya fi kowane lalacewa,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?
Kasashen Ketare

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?
Kasashen Ketare

Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?

September 28, 2025
Next Post
Firaministan Vanuatu: Tunanin Al’ummar Dan Adam Mai Kyakkyawar Makomar Bai Daya Ya Zo Daidai Da Burin Kasar Vanuatu

Firaministan Vanuatu: Tunanin Al'ummar Dan Adam Mai Kyakkyawar Makomar Bai Daya Ya Zo Daidai Da Burin Kasar Vanuatu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version