Kananan Manoma Mata Sun Bukaci Kara Yawan Kasafin Kudin Aikin Noma
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kananan Manoma Mata Sun Bukaci Kara Yawan Kasafin Kudin Aikin Noma

byAbubakar Abba
10 months ago
Manoma

Manoma mata a Jihar Ebonyi, sun bukaci matakan gwamnati uku na kasar nan, da su zuba jari mai yawan gaske a fannin noma. Har ila yau, sun yi nuni da cewa; hakan zai taimaka matuka wajen kawo karshen matsalar karancin abinci a fadin kasar.

Manoman sun kara da cewa, kara samun zuba jari a fannin zai kara yawan tattalin arzikin noma zuwa a kalla kashi shida cikin dari.

  • Yadda Barayin Amfanin Gona Ke Kassara Manoma
  • ‘Yan Bindiga Sun Kone Gonakin Manoma A Zamfara

Sun sanar da haka ne, a taron masu ruwa da tsaki kan kasafin kudi da jihar ta  Ebonyi ta ware wa fannin a 2025.

An gudanar da taron ne, bisa hadakar ma’aikatar aikin noma da kula da albarkatun kasa ta jihar da kuma kwamitin kasafin kudi na jihar tare da kungiyoyin mata na kananan manoma.

Kana, an samu nasarar aiwatar da taron ne tare da goyon bayan kungiyar ‘Actionaid’; wadda ke gudanar da ayyukanta a Nijeriya.

Bugu da kari, manoman sun kuma yi kira ga gwamnati da ta samar da tsare-tsare tare da kafa dokoki a kan yin amfani da magungunan kashe kwari da ke dauke da sinadaran da za su iya shafar kiwon lafiyar manoma.

Kazalika, sun yi kira ga majalisar dokokin jihar da ta tabbatar da an amince da kasafin kudin a kan lokaci da kuma yin amfani da dabarun kara bunkasa noma a jihar.

A cewarsu, yin hakan a kan lokaci; zai taimaka wajen rage yunwa da fatara, musamman don cika yarjejeniyar Maputo/Malabo da aka rattabawa hannu.

Sannan kuma, sun bukaci ‘yan majalisar da su tabbatar da cewa, sun mayar da hankali a fannin aikin noman; domin amfanin al’ummar mazabunsu.

Manoman, sun kuma shawarci ma’aikatar aikin noma ta jihar da hukumomin gwamnatin jihar, da su tabbatar sun fadada tuntuba da masu ruwa da tsaki a fannin aikin noma a yayin wanzar da kasafin kudin na badi.

Sun kuma bukaci a zuba jari na musamman, wajen sama wa manoma mata rance da kuma kayan aikin noma na zamani, musamman don rage yawan asarar da manoman ke yi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Gwamnan Shekarar 2024: Mallam Umar A. Namadi

Gwamnan Shekarar 2024: Mallam Umar A. Namadi

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version