Haruna Akarada">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Kanawa Sun Bayyana Ra’ayoyinsu Game Da Zaben Kananan Hukumomin Kano 

by Haruna Akarada
January 18, 2021
in LABARAI
2 min read
Kananan Hukumomin Jihar Kano
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

A ranar Asabar din da ta gabata, 16 ga Janairu, 2021, ne aka gudanar da zaben yankunan kananan hukumomi a dukkan fadin Jihar Kano. Wannan ya sa LEADERSHIP A YAU ta kewaya wasu mazabu, domin ganin yadda zaben ke gudana tare da jin ra’ayoyin mutane.

Babu shakka ra’ayoyi sun bambanta kan yadda muka ji daga bakin mutane daban-daban ta kowanne bangare. Akwai babbar mazabar Kaura-Goje, inda muka samu tattaunawa da wasu daga cikin wadanda suka halarci zaben.

 

Abdullahi Hadi Umar, daya ne daga cikin wadanda suka kada kuri’a a wannan filin makaranta, ya bayyana yadda zabe ke tafiya, inda ya ce ya yi nasa zaben kuma ya ga ana yin zabe lami-lafiya kalau sai dai rashin fitowar al’umma ne kawai, wanda wannan kuma yana nuni da cewa, a duba al’amuran matasa da kuma a tallafa musu, kuma a cewarsa, gaskiya wannan ya nuna cewa rashin aikin yi ya damu al’umma.

Shi kuwa Hon. Muhammad Sani Yau Nusa Kaura-Goje cewa ya yi, wannan zabe ana yin sa cikin kwanciyar hankali da nasara. Ya ce, tun da aka sa akwatin zaban nan daga safe zuwa yanzu babu wanda ya nuna wa wani ko dan yatsa, kuma ana ta kai-komo a cikin wannan fili babu wata matsala.

 

Shi kuwa Musa Muhammed Mabo cewa ya yi, zabe yana gudana kawai dai matsalar da aka samu ita ce rashin kawo kayan zabe da wuri, amma komai yana gudana kalau. Kuma cewa wannan zabe ba ‘yan adawa wannan ba gaskiya bane domin a wannan gurin akwai ‘yan jam’iyar PDP kuma suna wannan wajen kuma ga shi nan suna kare jam’iyarsu.

 

Shi kuwa Ta’ambo ya yi kira ga gwamnati da ta dinga taimakawa jama’a domin mutane suna cikin wani hali. “ Zuwanmu makarantar Dangana kuwa, nan ma mun hadu da Honarabul Ado Gambo Tsohon Kansila na mazabar Tudun Murtala, ya bayyana cewa an sami nasara domin daidai gwargwado an fito to wannan ma nasara ce.

 

A cikin wasu kuwa da ba su je wajen zaben ba, wani mai suna Labaran ya bayyana ra’ayinsa na kin zuwa wajen zaben, inda ya ce, ai ko ya je ko bai je ba tuni sun gama zabensu, don haka babu dalilin sa ya je ya sha wahalar banza.

Wata kuwa mai suna Halima ta ce ai ta yi amfani da wannan ranar wannan zaben, domin ta kwanta ta yi baccinta ya fi mata.

SendShareTweetShare
Previous Post

Borno Ta Ware Miliyan N624 Wajen Bai Wa Dalibai 23,776 Tallafin Karatu

Next Post

Nijeriya Ta Wajabta Wa Jami’an Diflomasiyya Mallakar NIN

RelatedPosts

Alkalin Kotun Koli, Ngwuta, Ya Rasu A Abuja

Alkalin Kotun Koli, Ngwuta, Ya Rasu A Abuja

by Haruna Akarada
13 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim Mai Shari’a Sylvester Ngwuta, alkalin kotun koli...

Tinubu Ya Bukaci Matasa Su Nisanci Bangar Siyasa

by Haruna Akarada
20 hours ago
0

Daga Bello Hamza, Jagoran jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu, ya...

E Call

Shirin Kula Da Zirga-zirgar Manyan Motoci Na ‘E-Call’ Zai Kawo Karshen Cunkoso A Tashar Jiragen Ruwan Nijeriya -Hadiza Bala Usman

by Haruna Akarada
20 hours ago
0

By Bello Hamza, An tabbatar wa masu hulda da tashoshin...

Next Post
Katin Zama Dan Kasa

Nijeriya Ta Wajabta Wa Jami’an Diflomasiyya Mallakar NIN

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version