Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RIGAR 'YANCI

Karamar Hukumar Gabasawa Gidan APC Ce – Garun Danga

by Muhammad
March 4, 2021
in RIGAR 'YANCI, Uncategorized
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Ibrahim Muhammad,

Shugaban Karamar Hukumar Gabasawa, Hon. Mahe Garba Garun Danga ya bayyana cewa Karamar Hukumar tasa tamkar gida ne ga jam’iyyarsu ta APC domin duk zabubbukan da aka yi a baya, babu wata kujera da jam’yyar ba ta yi nasara a kai ba.

Ya ce, saboda haka ma aikin sabunta rijistar jam’iyyar da ake yi, mutanen Karamar Hukumar Gabasawa suna tururuwan zuwa suna sabunta katin, duk da an dan sami akasi da katunan Karamar Hukumar ba su zo da wuri ba, amma yanzu da aka karbo ana yi, kuma jama’a nata zuwa suna karba.

Shugaban na Gabasawa ya yi kira ga jama’ar, Karamar Hukumar su ci gaba da ba su hadin kai domin duk abubuwa da suka yi a baya da nasarori da suka samu ba kokarinsu ko dabarar su ba ne Allah ne ya ba su iko suka aiwatar da abubuwa na ayyukan ci gaba bisa irin hadin kai da jama’a suka ba su, kuma cikin yardar Allah za su ci gaba da dorawa akai daga inda suka tsaya ta hanyoyi daban-daban na taimaka wa al’umma.

Ya yaba wa dan majalisarsu ta tarayya mai wakiltar Gabasawa da Gezawa, Hon. Nasiru Abdu Gabasawa bisa yadda yake taimaka wa ci gaban al’umma, ya yaba da irin tallafin da ya baiwa iyayen kasa Dagatai da Limamai da dalibai irin wannan ake bukata kawo hanyoyi da za a rika taimaka wa jama’a.

Hon. Mahe Garba Garun Danga ya kara yaba wa dan majalisar tarayyan da irin wannan gagarumar gudumawa da ya kawo, dama a tsarin dan majalisar ba wani wata da zai zo ba tare da ya aiko da kudi na tallafa wa jama’a daban-daban ba, mazaba-mazaba ana tallafa wa al’umma, wanda ba ma bayyanawa ake ba, sai dai su da suka sani.

Ya ce, yanayi Irin wannan na tara jama’a a tallafa musu a bayyane yanzu ya fara, amma gudumawa da yake baiwa jama’a aikin sa ne a kowane lokaci.

Hon. Mahe Garba Garun Danga ya yi kira ga al’ummar Kano su ci gaba da baiwa manufofin Gwamnatin Kano, karkashin Dokta Abdullahi Umar Ganduje goyon baya don ci gaba da ayyukan alkhairi da ake gudanarwa.

SendShareTweetShare
Previous Post

NDLEA Ta Kwace Bindiga 27 Daga Wasu Masu Laifi A Jihar Neja

Next Post

Gwamna Buni Ya Rantsar Da Sabbin Shugabanin Kananan Hukumomin Yobe

RelatedPosts

Gwamnatin Kaduna Ta Yi Wa Karnuka 6,250 Allurar Rigakafin Cutar Rabis

Gwamnatin Kaduna Ta Yi Wa Karnuka 6,250 Allurar Rigakafin Cutar Rabis

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Daga Bello Hamza, Abuja Gwamnatin jihar Kaduna ta samu nasarra...

Garkuwa

‘Yan Sanda Sun Kubutar Da Mutum 15 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Kaduna

by Muhammad
1 week ago
0

Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna, ta samu nasarar kubutar da...

Caca

Caca: An Kashe Mutum Uku Akan Naira 50 A Imo

by Muhammad
1 week ago
0

Daga Rabiua Ali Indabawa, An bayar da rahoton kashe samari...

Next Post
Gwamna Buni

Gwamna Buni Ya Rantsar Da Sabbin Shugabanin Kananan Hukumomin Yobe

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version