Karo Na 35 Ne Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Kammala Ziyararsa Ta Farko A Kowace Shekara A Afirka Cikin Nasara
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karo Na 35 Ne Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Kammala Ziyararsa Ta Farko A Kowace Shekara A Afirka Cikin Nasara

byCGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
Sin

“Ana sa ran zurfafa bunkasar dangantakar abokantaka mai moriyar juna tsakanin Sin da Afirka”, “Kasar Sin ta yi alkawarin ba da goyon baya ga kasashen Afirka wajen karfafa matakan tsaro”, “Kasar Sin na adawa da tsoma baki cikin harkokin cikin gidan kasashen Afirka”…wadannan kalamai ne da kafofin yada labaran Afirka da dama suka bayyana kan ziyarar da ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya kai nahiyar Afirka, wadda ya kammala a yau 11 ga wata.

Wadanda ke bibiyar harkokin diflomasiyya na Sin sun san cewa, ministan harkokin waje ya kan kai ziyararsa ta farko nahiyar Afirka a kowace shekara, al’adar da ta shafe shekaru 35 tana ci gaba da gudana. Bana ce ta cika shekaru 25 da kafuwar taron dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC) kuma shekara ta farko da aka fara aiwatar da sakamakon taron kolin na Beijing. Don haka ziyarar da ministan harkokin wajen kasar Sin ya kai kasashen Namibia, da Jamhuriyar Kongo, da Chadi da Najeriya a farkon wannan shekara, ba wai kawai ta maimaita abun da kasashen Sin da Afirka suka saba yi a baya, wato ministan harkokin wajen kasar Sin ya kan kai ziyararsa ta farko nahiyar Afirka a kowace shekara ba, har ma ta sa kaimi ga aiwatar da sakamakon da aka cimma na taron kolin Beijing.

A yayin wannan ziyararsa a Afirka, ministan harkokin wajen kasar Sin ya mai da hankali kan hadin gwiwa a fannonin tsaro da samun ci gaba da kasashen Afirka. Alal misali, kasar Sin ta ba da shawarar cewa, za ta ba da goyon baya ga kasashen Afirka wajen warware matsalolin Afirka ta hanyar Afirka, da kuma daukar kwararan matakai don taimakawa kasashen Afirka wajen daidaita batutuwan da suka haifar da rashin tsaro. Kasar Sin a shirye take ta daidaita karfinta da kasashen da abin ya shafa wajen kokarin samun damar yin hadin gwiwa a sabbin fannoni kamar makamashi mai tsafta, da samun ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba a fannin ma’adanai da hada-hadar kudi, da taimakawa kasashen Afirka wajen bin hanyar samun ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba da rage fitar iskar carbon. Akwai kalaman da ke cewa, bunkasuwar hadin gwiwar Sin da Afirka ba wani yunkuri ne na tilasta wa Afirka bukatunta ba. A maimakon haka, ta mayar da hankali kan mayar da martani ga buri da damuwar ci gaban Afirka bisa ka’idar samun moriyar juna da samun nasara tare. (Mohammed Yahaya)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
Uwargidan Tinubu Ta Kai Wa Gwamnan Jigawa Ziyarar Ta’aziyyar Rasuwar Mahaifiyarsa Da Ɗansa

Uwargidan Tinubu Ta Kai Wa Gwamnan Jigawa Ziyarar Ta'aziyyar Rasuwar Mahaifiyarsa Da Ɗansa

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version