Karramawar Shugaban Kasa Ta Kara Min Ƙaimi - Sadiya Farouq
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Karramawar Shugaban Kasa Ta Kara Min Ƙaimi – Sadiya Farouq

bySulaiman
3 years ago
Sadiya Farouq

Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, Hajiya Sadiya Umar Farouq
ta bayyana jin daɗin ta bisa karramawar da ta samu ta NEAPS, inda ta ce abin zai ƙara mata ƙaimi da jajircewa a aiki.

Minista Sadiya ta ce: “Wannan wani muhimmin zango ne, musamman a rayuwa ta, domin wannan karramawa shaida ce ƙarara ta gamsuwar da aka yi da ‘yan nasarorin da na samu a wajen ayyukan da na yi wa jama’a ya zuwa yanzu da kuma alhakin da aka ɗora mani a fagen ayyukan inganta rayuwa da jinƙai a cikin ‘yan shekarun nan.

  • Ambaliyar Ruwa: Ku Kwashe Jama’ar Da Suke Zaune A Yankunan Magudanun Ruwa — Sadiya Farouq

Daga nan sai ta bayyana cewa “ina so in ƙara miƙa matuƙar godiya ga mai girma Shugaban Ƙasa saboda damar da ya ba ni na yi wa ƙasa ta aiki a matsayin Ministar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa, sannan ta hanyar wannan muƙamin na yi ƙoƙarin bautata wa ɗimbin mutane marasa galihu waɗanda ke cikin buƙatar a inganta rayuwar su da taimakon jinƙai cikin gaggawa a faɗin ƙasar nan.

“Haka kuma ina godiya matuƙar gaske ga kamfanin ‘TBS Media’ da Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya da su ka ga dacewa ta har su ka ba ni wannan babbar kyauta ta NEAPS ta shekarar 2022 a ɓangaren ayyukan jinƙai, kuma su ka ɗora ni kan matakin shiga da’irar sauran manyan ‘yan Nijeriya waɗanda su ma aka karrama su tare da ni a yau.”

Ministar ta sha alwashin za ta ci gaba da yin bakin ƙoƙarin ta wajen yi wa ƙasar nan aiki wanda yin shi ne gudunmawar ta wajen taimakawa a tsamo Nijeriya daga cikin matsalolin da su ka addabe ta.

Mai taimaka wa ministar a fagen aikin jarida, Nneka Ikem Anibeze, ta yi ƙarin bayanin cewa wannan kyautar karramawa da aka yi saboda aiki ga jama’ar Nijeriya “manufar ta ita ce a karrama muhimman ayyukan da aka yi wa jama’a a Nijeriya ta hanyar gudunmawar da jama’a ɗaiɗaiku da jihohi da mutanen unguwa su ka bayar wajen shugabanci da aikin jama’a da jinƙai.”

In dai ba a manta ba, a ranar Juma’ar da ta gabata ne Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya jagoranci miƙa waɗannan kyaututtuka ga Minista Sadiyya da wasu mutum 44.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya
Rahotonni

Nijeriya A 65: ACF Da Afenifere Sun Yi Hannun Riga Kan Makomar Nijeriya

October 4, 2025
Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin
Rahotonni

Bashin Karatun Dalibai: Arewa Maso Yamma Ce Kan Gaba Wajen Cin Gajiyar Shirin

October 3, 2025
Next Post
NDLEA Ta Kama Wasu ’Yan Kwaya 4 Da Ake Nema Ruwa A Jallo Kan Mu’amala Da Miyagun Kwayoyi

NDLEA Ta Kama Wasu ’Yan Kwaya 4 Da Ake Nema Ruwa A Jallo Kan Mu’amala Da Miyagun Kwayoyi

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version