Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Kasafin 2021: Gwamnonin Arewa Maso Gabas Sun Koka Da Karancin Kasafin Gudanar Da Manyan Ayyuka A Shiyyar

by Muhammad
November 28, 2020
in LABARAI
4 min read
Gwamnonin Arewa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Khalid Idris Doya

 

samndaads

Gwamnonin Arewa Maso Gabas sun nuna takaicinsu da karancin kudaden gudanar da manyan ayyuka a shiyyar da aka ware a kasafin kudin 2021, su na masu neman majalisar kasa da ta sake waiwaye gami da nazarin kasafin domin tabbatar da adalci da daidaito a tsakanin shiyyoyin kasar nan.

 

 

Jawabin bayan taron da suka fitar na cewa: “Kungiyar ta bayyana takaici ganin duk da irin kalubalen ci gaba musamman a fannonin ayyukan raya kasa da shiyyar ke fuskanta, Naira biliyan 45.32 ne kacal aka ware don manyan ayyuka wa yankin a kiyasin kasafin kudin badi. Wanda hakan bai wuce kaso 0.035 cikin dari ba na kasafin kudin, wanda ya kai Naira triliyan 13.02. Wannan na nufin an yi watsi da shiyyar Arewa Maso Gabas.”

 

Don haka kungiyar ke kira ga majalisun tarayya su sake dubi kan kasafin kudin na badi don tabbatar da daidaito da tafiya da kowa. Ta kuma bayyana goyon baya ga ‘yan majalisun wakilai da na dattijan dake wakiktan shiyyar su dauki matakan gaggawa na ganin an yi gyara ga wannan rashin daidaito.

 

Kungiyar ta kuma koka kan rashin adalcin da ma’aikatar ayyuka da gidaje ta tarayya ke yi ta fuskar samar da hanyoyin mota. Ta kuma bayyana takaicin yadda ayyukan hanyoyin da aka bayar a yankin ke tafiyar hawainiya ko ma suka tsaya cak, inda ta yi kiran a gaggauta sake dubi kan halin ni ‘yasun da  kwangilolin da aka bayar a yankin suke ciki.

 

 

Kungiyar gwamnoni Arewa Maso Gabas da ta kunshi gwamnonin Adamawa da Bauchi da Borno da Gombe da Taraba da kuma Yobe, sun tattauna ne kan kalubalen da shiyyar ke fuskanta da kuma daukan matakan da suke ganin za a samu shawo kan wasu daga cikin matsalolin.

 

Kan lamarin tsaro a shiyyar, Kungiyar gwamnonin ta lura cewa ana samun ci gaba a sha’anin tsaro a yankin. Amma duk da haka, aika-aikar ‘yan kungiyar Boko Haram da na ‘yan bindiga, da barayin shanu da masu garkuwa da mutane na ci gaba da zama barazana ga ci gaba mai dorewa a yankin.

 

Duk da gwamnonin sun yaba wa kokarin jami’an tsaro a shiyyar, ta amince ta karfafa ‘yan sandan cikin al’umma tare da dafawa kokarinsu, kana sun nemi jami’an tsaron su kara himma domin karasa kakkabe ‘yan ta’adda a yankin.

 

Kungiyar ta kalailaice irin kalubalen da ilimi ke fuskanta a shiyyar, inda ta yanke shawarar tinkarar matsalar a kungiyance don farfado da sashin, musamman ma ilimin firamare, inda ta yanke shawarar kirkiro hukumar kula da ilimi ta shiyyar arewa maso gabas.

 

Kungiyar gwamnonin ta kuma jaddada himmatuwar ko wace jiha a shiyyar wajen karfafa dokar ilimin bai daya daga tushe ta UBEC don tabbatar da cewa daukacin yaran yankin sun samu damar samun ilimi daga tushe.

 

“Kungiyar ta bayyana bukatar karfafa hada karfi da karfe tsakanin jihohin shiyyar don tinkarar matsaloli da bukatun da za su amfani jihohin yankin, inda gwamnonin yankin suka amince su nada mashawarta na musamman kan sha’anin karfafa alaƙa tsakanin jihohin shiyyar.”

 

Jawabin matsayar bayan taron na kuma nuni da cewa, kungiyar ta nazarci batun kudin tallafin farfado da tattalin arziki bayan illar da annobar Korona ta janyo, wadanda suka kai Naira triliyan 2.3. yaayin da take jinjinawa gwamnatin tarayya bisa kirkiro da wannan tsari, ta bukaci a tabbatar da adalci da daidaito wajen rabon tallafin, musamman bisa la’akari da kalubalen tattalin arziki da zamanta kewa dake addabar yankin.

 

Daga bisani karshen taron ya cimma matsayar cewa taron da za ta gudanar a nan gaba zai guda ne a tsakanin ranakun 3 da 4 ga watan Maris na badi a jihar Bauchin Yakub

SendShareTweetShare
Previous Post

Maina: Kotu Ta Ba Da Belin Sanata Ndume

Next Post

Tsaron Kasa: Rundunar Sojin Sama Ta Jaddada Kudurinta Na Kare Nijeriya

RelatedPosts

Buba Marwa Ya Zama Sabon Shugaban Hukumar NDLEA

Buba Marwa Ya Zama Sabon Shugaban Hukumar NDLEA

by Muhammad
9 hours ago
0

Daga Abba Ibrahim Gwale, Shugaban kasa Muhammad Buhari ya amince...

Kananan Hukumomin Jihar Kano

Yau Za A Yi Karon Batta A Zaben Kananan Hukumomin Jihar Kano

by Sulaiman Ibrahim
19 hours ago
0

 Jam’iyyu 11 ne za su fafata PDP Kwankwasiyya ta ce,...

Sojoji

Tsofaffin Sojoji Sun Nemi Karin Kudin Fansho

by Sulaiman Ibrahim
19 hours ago
0

Kungiyar tsofaffin sojoji ta kasa reshen jihar Anambra ta bukaci...

Next Post
Tsaron Kasa: Rundunar Sojin Sama Ta Jaddada Kudurinta Na Kare Nijeriya

Tsaron Kasa: Rundunar Sojin Sama Ta Jaddada Kudurinta Na Kare Nijeriya

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version