Aabubakar Abba">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home NOMA

Kasafin 2021: Sanata Ya Soki Buhari Kan Yi Wa Noma Kwauron Hannu

by Aabubakar Abba
November 23, 2020
in NOMA
2 min read
Noma Kwauron Hannu
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Mataimakin Shugaban Marasa Rinjaye na Majalisar Dattawa, Emmanuel Bwacha, ya soki Shugabannin Nijeriya karkashin jagorancin Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari kan rashin kebewa fannin aikin noman kasar nan isassun kudade.

Emmanuel Bwacha ya yi sukar ce lokacin da Ministan Noma da Raya Karkara, Sabo Nanono, ya bayyana a gaban kwamitin Majalisar Dattawa kan harkar noma don kare kasafin kudin ma’aikatar na 2021.

samndaads

Kasafin kudin, wanda aka aike wa da majalisar kasa, yana jiran ‘yan majalisar su amince har ila yau, kasafin kudin da aka gabatar wa bangaren, kasa da kashi biyu cikin 100 na kasafin kudin 2021, ya sabawa da yarjejeniyar taron harkar noma na Afrika da ake kira taron Maputo.

A shekarar 2003, Nijeriya na daga cikin kasashen da suka shiga yarjejeniyar ta Maputo wacce ta umarci dukkan kasashe yayan kungiyar su kebe akalla kashi 10 na kasafin kudinta na shekara-shekara ga harkar noma.

Yarjejeniyar takunshi muhimman shawarwari da dama, daga cikinsu akwai jajircewar akalla kebe kashi 10 na kasafin kudin kasa ga harkar noma da ci gaban karkara a cikin shekaru biyar.

Sai dai, tun lokacin da aka rattaba hannu kan yarjejeniyar, Nijeriya ba ta taba cimma burin da aka sa gaba na kebewa fannin noma da kudade masu ya wa ba.

Mista Bwacha ya so ki shugabannin yanzu da na baya game da cin amanar da yankin ta hanyar talaucin kudaden da aka kebewa, inda ya kara da cewa, mun gaza saboda wannan bayanin da aka yi a karkashin Tarayyar Afirka wacce kuma an yi ta ne a karkashin gwamnatocin kasashen da suka shiga yarjejeniyar.

Mataimakin Shugaban Marasa Rinjaye na Majalisar Dattawa, Emmanuel Bwacha, ya kara da cewa, ba ma a kasafin kudi na kasa daya ba mun kuma iya daukar kashi 7 cikin dari.

Ministan Aikin Gona da Raya Karkara Alhaji Sabo Na Nono wanda ke kan kujerar shugabancin Bankin Raya Kasashen Afirka ya bayyana cewa, ‘yan Nijeriya suna ta fa ta sosai kan ci gaban fannin noman kasar nan, inda ya kara da cewa, an yinkokari don wayar da kanmu game da fadada tattalin arziki.

A cewar Ministan Aikin Gona da Raya Karkara Alhaji Sabo Nanono, na damu saboda wasu mutane sun dora laifin kan gwamnatin daga 1999 har zuwa yau, inda ya kara da cewa, na ambaci hakan ne saboda dukkan shugabanin da ministocin da da suka yi aiki tsawon shekaru ba su iya nuna kwazo na gaske ba saboda ana zuba kudin a bangaren noma.

Ministan Aikin Gona da Raya Karkara Alhaji Sabo Nanono ya kara da cewa, yaushe ne za mu dauki wannan da muhimmanci watakila a matsayin al’umma ko a matsayin majalisa, tare da zartarwa.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Amfani Da Kayan Ketare Ya Kashe Tattalin Arzikin Nijeriya – Minista

Next Post

Abinda Yakamata Ka Sani Game Da Rancen Da Nijeriya Za Ta Karbo Daga Brazil

RelatedPosts

Shanu

Manyan Motoci 60 Ke Zuwa Kasuwar Sayar Da Shanu Ta Wudil A Duk Sati

by Aabubakar Abba
15 hours ago
0

Akwai ksauwannin sayar da Shanu da dama a Nijeriya, amma...

Rogo

Muna Bukatar Takin Zamani –Manoman Rogo A Kwara

by Aabubakar Abba
5 days ago
0

Manoman Rogo a jihar Kwara sun yi kira ga gwamnatin...

Kananan Manoma

Kananan Manoma Sun Bukaci Bashi Daga CBN

by Aabubakar Abba
5 days ago
0

Wasu daga cikin kananan manoman a kasar nan, sun bukaci...

Next Post
Brazil

Abinda Yakamata Ka Sani Game Da Rancen Da Nijeriya Za Ta Karbo Daga Brazil

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version