Kasar Sin A Matsayin Katafariyar Cibiyar Kere-Keren Mutum-Mutumi A Duniya
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin A Matsayin Katafariyar Cibiyar Kere-Keren Mutum-Mutumi A Duniya

byCGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
Sin

Zamanin da muke ciki na samun ci gaba cikin hanzari ta fuskar kimiyya da fasaha yana ci gaba da shaida sabbin kere-kere da fasahohi na kara inganta gudanar da ayyuka a sassa daban-daban na rayuwar bil’adama. Daya daga cikin sassan da suke daukar hankali shi ne sashen sarrafa mutum-mutumi na kasar Sin.

Cibiyar Morgan Stanley da ke nazarin hidindimun kudi da sauran harkokin sarrafa dukiya mai hedkwata a birnin New York na Amurka, ta fitar da wani rahoto a watan Fabrairun da ya gabata game da masana’antun sarrafa mutum-mutumi a duniya, inda ya bayar da bayanai game da yanayin samar da mutum-mutumi a duniya. Rahoton ya nuna yadda kasar Sin ke taka rawar gani a fagen, saboda habakar da take samu wajen kere-keren mutum-mutumin musamman masu siffofin bil’adama.

  • Xi Jinping Ya Halarci Bitar Tawagar Lardin Jiangsu
  • An Koya Min Girmama Mata – Akpabio Ya Musanta Zargin Cin Zarafin Natasha

Rahoton na Morgan ya nuna cewa, kamfanonin kasar Sin ne suke da kashi 63 a cikin dari na dukkan mutum-mutumin da ake samarwa a duniya. Kana daga cikin adadin kamfanonin da ake da su a masana’antar, kashi 73 cikin dari a yankin Asiya suke, kuma kasar Sin ke da kashi 56 cikin dari a cikin adadin nasu.

Tun fiye da shekara 10 da suka gabata, kasar Sin ke kara samun habakar masana’antar kera mutum-mutumi. Rahoton da Kungiyar Samar da Mutum-mutumi ta Duniya (IFR) ta fitar game da harkokin kera mutum-mutumi na shekarar 2024, ya nuna cewa, kasar Sin ta yi wa kowa nisa a duniya wajen zama babbar katafariyar kasuwar mutum-mutumi ta duniya bisa yadda ta yi nasarar kakkafa masana’antun bangaren guda 276, 288 a shekarar 2023. Wannan ya sa kasar ta mallaki kashi 51 cikin dari na daukacin adadin masana’antun sashen da aka kafa a duniya.

Har ila yau, zuwa shekarar 2024, bayanan mahukuntan kasar Sin sun nuna a watan Yulin shekarar, kasar ta habaka fiye da sassa masu inganci da ke da alaka da mutum-mutumi 190,000, wanda hakan ke nuna kasar ce ke da kaso biyu bisa uku na daukacin wadanda ake da su a duniya.

Hakika, kasar Sin ta nuna bajinta a kan habakar da take samu a fagen kere-keren mutum-mutumi musamman ma a yayin bikin bazara na shekarar 2025 inda aka jero wasu mutum-mutumi 16 suka gudanar da raye-raye masu kayatarwa a wani bangare na shagulgulan jajibirin bikin. Yadda mutum-mutumin suka rika kwarkwasa da rawa da juyi ya yi matukar birge ’yan kallo na ciki da wajen kasar.

Bugu da kari, a karon farko, mutum-mutumi za su shiga a dama da su a wasan gudun fanfalakin da za a gudanar cikin watan Afrilu mai zuwa a Beijing, babban birnin kasar Sin, inda ake sa ran mutum-mutumin nan da aka saka masa fasahar kirkirarriyar basira ta AI, Tian Kung wanda cibiyar bunkasa kere-keren mutum-mutumi masu kirkirarriyar basira ta kasar Sin ta kera, na daga cikin wadanda za a fafata gudun da su. Duka dai, wannan yana kara fayyace ci gaban da kasar Sin take samu ne a fannin. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Next Post
Lin Jian Ya Yi Bayani Kan Takardar Bayani Game Da Shawo Kan Sinadarai Masu Alaka Da Sinadarin Fentanyl Ta Sin

Lin Jian Ya Yi Bayani Kan Takardar Bayani Game Da Shawo Kan Sinadarai Masu Alaka Da Sinadarin Fentanyl Ta Sin

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version