Kasar Sin Karfi Ce Ta Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Karfi Ce Ta Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya

byCGTN Hausa
2 years ago
Sin

A duniyarmu ta yau, kasar Sin ta kasance amintacciyar kasa, mai daukar nauyi da dawainiyar tsarin harkokin duniya dake cike da rashin kwanciyar hankali da daidaito, da bude kofa ga dukkan nau’o’in hadin gwiwar bangarori daban-daban. Yayin da kasashen yammacin duniya ke kokarin raba gari da kasar Sin, da ma kokarin kawo tsaiko ga ci gabanta da dunkulewar duniya baki daya, yanzu kasar Sin ce ke kokarin kira da tabbatar da daidaito tsakanin bangarori daban-daban da inganta tsarin duniya.

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gabatar da wani muhimmin jawabi mai taken “Taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da zaman lafiya a duniya mai cike da tashin hankali” a taron tsaro na Munich da aka gudanar a ranar 17 ga watan Fabrairu.

  • Wang Yi Ya Yi Tir Da Karairayin Da Ake Yi Game Da Xinjiang A Munich
  • Al’ummar Afirka Ta Yi Maraba Da Sakon Xi Jinping Ga Taron AU Karo Na 37

Taron Tsaro na Munich (MSC) taro ne na shekara-shekara kan manufofin tsaro na kasa da kasa a birnin Munich na Jamus. Asalin taken ita ce: “Zaman lafiya ta hanyar tattaunawa”, kuma taron na wannan shekara ya maida hankali kan ko kasashen duniya sun shirya samar da zaman lafiya a aikace ko za su ci gaba da maganar baka ne kawai?

Kasar Sin mai fada da cikawa, ta ba da gudummawar rundunar wanzar da zaman lafiya mafi girma duniya kuma kasa ta biyu da ta fi ba da gudummawar kasafin kudin Majalisar Dinkin Duniya. Ta yi alkawarin cika alkawuran COP28, da tafiyar da harkokin kirkirarriyar basira wato AI na duniya, da kuma zama jigon habaka harkokin duniya. Kasar Sin ta yi kira da a tsagaita bude wuta a Ukraine da Falasdinu. Wannan karin sauke nauyin tabbatar da zaman lafiya da ya rataya a wuyan kasashen duniya yana tafiya kafada da kafada da karfin kasar Sin da tasirinta a cikin al’ummar duniya, bisa ci gaban tattalin arzikinta.

Tabbatar da tsaro a duniya ga kowa da kowa yana nufin kwarewa wajen “aiki da cikawa”. Hakan zai faru ne a lokacin da kasashen duniya suka hade waje guda domin tabbatar da tsaro na gama gari, ba wai a bar wata kasa da aikin tabbatar da tsaron duniya yayin da wasu kasashen ke mata zagon kasa ba. Kudaden da aka kashe kan aikin soji a duniya ya karu zuwa dala biliyan 2240 a shekarar 2022 kuma yana ci gaba da haurawa kawo yanzu, kamar yadda lamarin tsaro ke ci gaba da tabarbarewa a duniya. Saboda ba a kasashe wadannan kudaden ta hanyoyin da suka dace ba, shi ya sa kwalliya ba ta biya kudin sabulu ba. An kashe kudaden ne bisa son ran kasashen yamma cike da rashin amana game da hakikanin manufarsu da muradunsu, hakan ya sanya ministan harkokin wajen kasar Sin Wang yi, bai kammala jawabinsa ba sai da ya jaddada tafiyar da harkokin diflomasiya bisa amana.

Don haka, a mahangar kasar Sin, hanyar da ta dace ga amincewa da juna ita ce hanyar bayyana irin gudummawar da Sin ke bi wajen daidaita harkokin duniya, da bukatunta, da kiyaye jajayen layuka masu nasaba da tashin hankali. (Muhammed Yahaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa
Daga Birnin Sin

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Next Post
Ministan Labarai

Tinubu Ba Zai Yi Murabus Ba, inji Ministan Yaɗa Labarai 

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version