Kasar Sin Mai Fada Da Cikawa
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasar Sin Mai Fada Da Cikawa

byCGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Sin

A farkon wannan mako ne, hukumar Kwastam ta birnin Changsha na lardin Hunan, ta ba da izinin shigar da naman rago daga kasar Madagascar cikin kasar Sin, wanda shi ne karo na farko da aka shigar da nama daga nahiyar Afrika cikin kasar Sin, lamarin dake zaman wata muhimmiyar nasara ga cinikayyar nama tsakanin Sin da kasashen Afrika.

 

Wannan nasara na zuwa ne a daidai lokacin da aka kammala taron koli na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afrika wato FOCAC, dake mayar da hankali kacokan kan kyautata dangantakar Sin da kasashen Afrika da al’ummominsu. Kuma karkashin wannan hadin gwiwa, batun bunkasa cinikayya daya ne daga cikinsu.

  • Xi Jinping Ya Taya Murnar Ranar Malamai Ta Kasar Sin
  • Mataimakin Firaministan Sin Ya Karfafa Gwiwar Kamfanonin Waje Da Su Shiga Aikin Sin Na Neman Samun Bunkasuwa Mai Inganci

Kasashen Afrika sun sha bayyana fatansu na cin gajiyar babbar kasuwar kasar Sin ta hanyar shigo da kayayyakinsu kasar. Hakika ganin wannan labari na shigowar naman rago na kasar Madagascar cikin kasar Sin, abun farin ciki ne. Duk da cewa a bara aka daddale wannan yarjejeniya, lamarin ya yi nuni da cewa, kasar Sin ta cika alkawarinta na bude kofa ga kasashen Afrika, haka kuma manuniya ce cewa, za a ga tarin sakamakon da aka cimma yayin taron FOCAC a aikace.

 

Kamar yadda ministan kula da harkokin cinikayya ta Nijeriya ta bayyana, cinikayya wata babbar hanya ce ta bunkasa tattalin arziki da zaman takewa da ma cudanya da fahimtar juna tsakanin bangarori da dama, inda ta ce cinikayya tsakanin Sin da Nijeriya, ya taka muhimmiyar rawa a wadannan bangarori a kasarta.

 

Ba samun kudin shiga kadai ba, bude kofar da Sin ta yi ga kasashen Afrika don su kawo kayayyakinsu, ya kara tabbatar da cewa da gaske take tana da muradin ganin dukkan bangarori sun ci moriyar juna, kana an samu ci gaba na bai daya. Haka kuma fadadar cinikayya tsakaninsu, ya kara mu’amala da dankon zumunta a tsakaninsu.

 

Ina da yakinin cewa, tabbatuwar yarjejeniyar shigo da karin kayayyakin kasashen Afrika cikin kasar Sin, ciki har da gyadar Nijeriya, za ta kara aminci da fahimta da dankon zumunta tsakanin al’ummominsu, haka kuma za ta bunkasa tattalin arzikin bangarorin biyu domin samun ci gaba na bai daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Next Post
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 6 Cikin Dari A Watannin 8 Na Farkon Bana

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 6 Cikin Dari A Watannin 8 Na Farkon Bana

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version