Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home DAGA BIRNIN SIN

Kasashen Afirka Na Ci Gaba Da Karbar Alluran Riga Kafi Daga Shirin COVAX

by Sulaiman Ibrahim
March 10, 2021
in DAGA BIRNIN SIN
2 min read
Kasashen Afirka Na Ci Gaba Da Karbar Alluran Riga Kafi Daga Shirin COVAX
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Ibrahim Yaya

Yayin da kasashe masu tasowa suka fara amfani da alluran riga kafin COVID-19 karkashin shirin nan na COVAX, da ma tallafin alluran riga kafin COVID-19 daga kasashe kamar kasar Sin, akwai bukatar a yiwa amfani da wadannan allurai yadda ya kamata, a kokarin ganin bayan cutar har ma a kai ga farfadowar tattalin arzikin duniya.
Kasar Ghana ce kasa ta farko a nahiyar Afirka da ta fara amfana da riga kafin karkashin shirin na COVAX, inda ta karbi kimanin alluran riga kafi 600,000 na kamfanin AstraZeneca, ita ma Najeriya ta karbi kasonta na farko na alluran riga kafin COVID-19 daga shirin na COVAX, a kokarin da mahukuntan kasar ke yi na dakile wannan annoba. Ana sa ran Najeriya za ta karbi allurai miliyan 16 a rubu’i na farko na bana, yayin da aka jinkirta kason da kasar Zimbabwe za ta samu karkashin shirin na COVAX zuwa watan Mayu.
Sauran kasashen Nahiyar ta Afirka da suka karbi riga kafin na COVAX, sun hada da Uganda da Habasha da Rwanda, da Jamhuriyar demokiradiyar Congo, da Gambia, da Angola, da sauransu.
Sai dai ba a nan take ba, wai an danne Bodari a ka, duk da alluran riga kafi gami da matakan da yaki da cutar da kasashe suke dauka, akwai bukatar su ma al’umma su bayar da hadin kai ta hanyar karbar riga kafi da martaba matakan lafiya na yaki da wannan annoba. Idan kana da kyau to, ka hada da wanka.
Kamar yadda ministan wajen kasar Sin Wang Yi ya fada yayin taron manema labaran da aka shirya a Lahadin da ya gabata a yayin taron majalisar wakilan jama’ar kasar dake gudana a birnin Beijing, fadar mulkin kasar Sin, bai kamata kasashen duniya su riga siyasantar da hadin gwiwar samar da alluran riga kafin annobar COVID-19 ba, da ma yadda wasu kasashe ke kokarin mallake alluran riga kafin, maimakon samar da su ga kasashe mabukata, musamman kasashe masu tasowa. Domin ta haka ne kadai, za a ga bayan wannan annoba baki daya. (Ibrahim Yaya)

SendShareTweetShare
Previous Post

Sin: Ya Kamata A Gudanar Da Bincike Kan Cibiyar Nazarin Kwayoyin Halittu Ta Fort Detrick

Next Post

Shafin Farko: Leadership A Yau Laraba 10 Ga Watan Maris 2021

RelatedPosts

Ci Gaban Kasar Sin A Fannin Fasaha Ba Ya Tsoron Danniyar Amurka

Ci Gaban Kasar Sin A Fannin Fasaha Ba Ya Tsoron Danniyar Amurka

by Sulaiman Ibrahim
19 hours ago
0

Daga Bilkisu Xin A ranar 8 ga wata, ma’aikatar kasuwanci...

Takunkuman Amurka Da Birtaniya Kan Sin Sun Keta Dokokin Kasa Da Kasa

Takunkuman Amurka Da Birtaniya Kan Sin Sun Keta Dokokin Kasa Da Kasa

by Sulaiman Ibrahim
19 hours ago
0

Daga CRI Hausa Tsohon Jakadan Italiya a kasar Sin, Alberto...

Masanan Sin Da Afirka Suna Fatan Za A Kara Yin Mu’amalar Al’adu Da Juna

Masanan Sin Da Afirka Suna Fatan Za A Kara Yin Mu’amalar Al’adu Da Juna

by Sulaiman Ibrahim
19 hours ago
0

Daga CRI Hausa Kwalajin nazarin harkokin Afirka na kasar Sin,...

Next Post
Shafin farko

Shafin Farko: Leadership A Yau Laraba 10 Ga Watan Maris 2021

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version