Kasashen Dake Kewayen Tekun Pasifik Suna Da Ikon Neman Diyya Daga Gwamnatin Japan Kan Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Ruwa Cikin Teku
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Dake Kewayen Tekun Pasifik Suna Da Ikon Neman Diyya Daga Gwamnatin Japan Kan Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Ruwa Cikin Teku

byCMG Hausa
2 years ago
Nukiliya

A kwanakin baya a jere, kasashen dake kewayen tekun Pasifik sun yi tir da matakin gwamnatin kasar Japan na zubar da ruwan dagwalon nukiliya ta Fukushima cikin teku.
A ganin wadannan kasashe ciki har da tsibirin Marshall wadanda ke fama da mummunar matsalar gurbatar muhalli sanadiyar nukiliya, matakin gwamnatin Japan a wannan karo ya sake sanya su cikin matukar damuwa.

Masanan da abin ya shafa sun yi nuni da cewa, bai kamata kasashen dake kewayen tekun Pasifik su daidaita matsalar da kansu, su dandana mummunan sakamakon da ya biyo bayan matakin gwamnatin Japan ba, suna da ikon neman diyya daga gwamnatin Japan game da wannan batu.

  • Tarihi Zai Dorawa Japan Alhakin Sakin Gurbataccen Ruwan Nukiliya Zuwa Teku

A halin yanzu, akwai yarjejeniyoyi da dama da suka yi bayani game da yadda wata kasa ta zubar da gurbataccen abun nukiliya a cikin teku. Kasar Japan ta daddale yarjejeniyoyin kasa da kasa da dama ciki har da yarjejeniyar kula da tekun da babu wata kasa da ta mallaka. Yanzu dai kasar Japan ta sabawa yarjejeniyoyin, babu shakka za ta dauki alhakinta ta kuma biya diyya ga kasashen dake kewayen tekun Pasifik.

Ban da haka kuma, kotun hukunta manyan laifuffuka ta duniya ta taba yanke hukunci ga kasar Canada daga shekarar 1938 zuwa 1941, saboda sinadarin sulfur dioxide da kamfanin sarrafa karafa na Trail na kasar Canada ya fitar ya kawo illa ga jihar Washington ta kasar Amurka, don haka aka bukaci kasar Canada ta biya Amurka diyya. Ana daukar wannan shari’a a matsayin tushen dokokin kasa da kasa, domin biyar alhakin kasa kan gurbatar muhalli a sauran kasashe bisa dokokin kasa da kasa.

Ana iya ganin cewa, kasashen da ke gabar tekun Pasifik na iya yin la’akari da wadannan shari’o’i, da kuma daukar mataki na kimiyya kan tabbatar da illolin da ruwan dagwalon nukiliya ta Fukushima ya haifa musu, su kai kara don neman diyya daga kasar Japan, da kare hakki da muradunsu.

Har kullum gwamnatin kasar Japan tana ikirarin tafiyar da harkokin teku bisa doka, amma yanzu ta gurfanar da kanta a gaban kotu. Za a yanke mata hukunci, kana kasashen dake gefen tekun Pasifik za su samu diyya daga wajenta domin wannan batu. (Zainab)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
Sin Ta Bukaci Kasashen Duniya Da Su Dauki Matakin Dakatar Da Japan Daga Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku

Sin Ta Bukaci Kasashen Duniya Da Su Dauki Matakin Dakatar Da Japan Daga Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Cikin Teku

LABARAI MASU NASABA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version