Kasashen Sahel Na Bukatar Agaji Domin Yaki Ta’addanci -Rasha
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Sahel Na Bukatar Agaji Domin Yaki Ta’addanci -Rasha

byRabi'u Ali Indabawa
2 months ago
Rasha

Rasha ta yi kira ga kasashen duniya su hada karfi da karfe wajen taimakon hadakar kasashen Alliance of Sahel States wato AES domin ba su taimakon da suke bukata a yakin da suke yi da matsalar tsaro.

Kasashen AES din su ne Mali da Burkina Faso da kuma Nijar wadanda suke karkashin mulkin soja bayan shugabannin mulkin kasashen sun hambarar da gwamnatin fararen hula.

  • Hadin Tuwon Dawa
  • Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta

Kafar Actualite.bf mai zaman kanta ne ta ruwaito cewa Rasha ta gabatar da wannan kokon baran ne a jawabinta ga kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya, inda wakilinta na dindindin, Dmitry Chumakob ya ce kasashen na bukatar agajin tsaro.

“Domin samun dawwamammen zaman lafiya, ya kamata kasashen duniya su ba kasashen Mali da Burkina Fasp da Nijar gudunmuwa,” in ji Chumakob.

Ya kara da cewa, “kasashen Afirka din ne da kansu suka fi sanin yadda za su magance matsalolin da suke fuskanta, kuma su ne suka fi sanin yadda za su yi yaki da matsalar tsaro da kuma hanyoyin inganta dimokuradiyya da tattalin arzikinsu.”

Rasha dai ta zama babbar kawar kasashen na AES, wadanda ke jan jikinsu daga wasu kasashen na yamma, inda Moscow ta kuduri aniyar taimakon kasashen wajen yaki da masu tayar da kayar baya.

 

Nijer Ta Ceto ‘Yan Gudun Hijira Da Suka Makale A Libya

Sojojin Jamhuriyar Nijar sun samu nasarar ceto ‘yancirani guda 50 da suke makala a sahara a hanyarsu ta tafiya kasar Libya.

RFI ta ruwaito cewa mutanen sun makale ne a kusa da bakin iyakar shiga kasar ta Libya bayan motarsu ta lalace a ranar 10 ga watan Agusta.

“Motarsu ta lalace ne a hanyarsu ta tafiya Libya, kasar da ake ratsawa domin tafiya kasashen turai. A ciki akwai fasinjoji 44 kuma motar tana tafiya ne a hanyar Madama-Dao da ke arewacin Nijar a lokacin da ta lalace, ta tsaya cak,” in ji rahoton na RFI.

Daga baya ne aka shiga neman motar, inda sojojin suka samu nasarar ceto su, sannan aka kai su garin Madama, inda ake cigaba da kula da su.

Sai dai har yanzu ba a tabbatar da asalin kasashen da mutanen suka fito ba, da kuma asalin kasar da suke shirin zuwa.

 

M23 Ta Musanta Zargin Kashe Gomman Fararen Hula A Kudancin Kibu

Kungiyar ‘yantawaye ta M23 a Congo ta musanta zarginta da ake yi da kashe gomman fararen hula a Kudancin Kibu na kasar, sannan kuma ta nanata cewa zarginta da ake yi da amfani da kananan yara a yaki kanzon kurege ne.

Kakakin M23, Willy Ngoma ne ya bayyana wa BBC haka, inda ya ce ko kadan ba ya cikin tsarinsu kai farmaki kan fararen hula.

“Ba ma kashe fararen hula. Ta yaya za mu kashe ‘yankasa, wadanda muke fafutikar karewa?

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Next Post
UNICEF Ya Jaddada Muhimmancin Yi Wa Yaran Afirka Rajistar Haihuwa

UNICEF Ya Jaddada Muhimmancin Yi Wa Yaran Afirka Rajistar Haihuwa

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version