Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Katsina Za Ta Kafa Kwamitin Kidayar Yaran Da ’Yan Bindiga Su Ka Mayar Marayu

by Muhammad
December 1, 2020
in RAHOTANNI
2 min read
kidayar
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Sagir Abubakar, Katsina

 

samndaads

Gwamnatin jihar Katsina za ta kafa kwamiti da zai gudanar da kidaya ga dukkan yara na wadanda yan bindiga suka kashe iyayensu a fadin jihar nan.

Gwamna Aminu Bello Masari ya sanar da hakan a lokacin da ya karbi bakuncin shuwagabannin kungiyar yansintiri na kasa a karkashin jagorancin babban kwamanda na kungiyar Dr. Usman Muhammad Jahun da Isuka kawo mashi ziyara. Kamar yadda ya ce yunkurin zai taimaka ma gwamnatin jiha ta fiddo da hanyoyin da za ta taimaka ma yaran. Gwamnan ya yi la’akari da cewa barin irin wadannan yaran haka nan zai iya haddasa wani abu.

Gwamnan jihar ya yi la’akari da cewa shigowar makamai da miyagun kwayoyi a kasar nan shi ne babban abun da ya ke taimakawa wajen aikace-aikacen yanbindiga.

Don haka, ya bukaci shugabancin kungiyar yansintirin musmaman wadanda suke a yankunan kan iyaka da jihar da su zama masu sanya idanuwa kuma su kai rohoton shigowar irin wadannan haramtattun kayayyakin a wasar nan ga hukumomi mafi kusa da su.

Wannan kamar yadda ya ce kari ne bisa ga aikce-aikce wasu da su ke kiran kansu yan sakai, wadanda suke zuwa daga wasu wurare su kai hari ga jama’a da sunan suna zarginsu da aiakce-aikace na ynabindiga.

Gwamnan ya kara jaddada kukurin gwamnati na taimakawa duk wata kungiyar da take da niyyar taimakawa wajen tabbatar da tsaro a jihar nan. Tun farko, babban kwamandan kungiyar yansintiri ta kasa Dr. Usman Muhammad jahun ya jaddada kudurin kungiyar domin taimakawa wajen kawar da yanbindiga a jihar nan.

Kamar yadda ya ce kungiyar za ta turo yayanta daga fadin kasar nan domin hada karfi da fiye da yayan kungiyarta yansintiri dubu ishirin da shidda da ke jihar nan domin kawar da aikace-aikacen yanbindiga a cikin watannin ukku.

Ya yi roko gwamnati da ta tallafama kungiyar da mota da kuma ofis domin samun damar gudanar da ayyukansu na sintiri yadda ya dace. Dr. jahun ya yi roko ga gwamnatin jiha da ta yi wata doka da za ta samar da yanayi mai kyau na aiki ga kungiyar kamar yadda wasu jihohin kasar nan suka yi.

SendShareTweetShare
Previous Post

Shugaban Hukumar Alhazai Kiristoci Ya Ziyarci Gwamna Masari

Next Post

’Yan Adawa Ne Ke Daukar Nauyin Rikici Don Zubar Wa Buhari Mutunci – DCN

RelatedPosts

Garban

Garban Kauye Farawa Ne Allurar Dinke Barakar Kumbotso – Muslihu Yusuf Ali

by Muhammad
17 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana zaben Sabon shugaban Karamar...

Harkokin Noma

Sarkin Noma Ya Shawarci Gwamnatin Tarayya Ta Kara Kokari Wajen Gyara Harkokin Noma

by Muhammad
17 hours ago
0

Daga Bala Kukkuru, Sarkin Noman Jihar Kano, Alhaji Yusuf Umar...

Kwazon Tambuwal

Hobbasar Kwazon Tambuwal Na Fara Biyan Albashi Daga Haraji A 2023

by Muhammad
2 days ago
0

Daga, Sharfaddeen Sidi Umar, Gwamnatin Jihar Sakkwato a karkashin jagorancin...

Next Post
'Yan adawa

’Yan Adawa Ne Ke Daukar Nauyin Rikici Don Zubar Wa Buhari Mutunci – DCN

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version