Kiraye-kirayen Maye Ganduje Da Kwankwaso: Dattawan APC Sun Mayar Da Martani
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kiraye-kirayen Maye Ganduje Da Kwankwaso: Dattawan APC Sun Mayar Da Martani

byYusuf Shuaibu
2 years ago
Kwankwaso

Ana ci gaba da kiraye-kiraye ga Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu kan ya cire shugaban jam’iyyar APC na kasa, Abdullahi Uamar Ganduje tare da yawo tsohon gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso.

Wannan lamari ya yi tsamari ne lokacin da matasan jam’iyyar APC na Jihar Kano suka bukaci Tinubu ya tabbatar ya janyo Kwankwaso a cikin jam’iyyar APC muddin yana so ya samu gagarimin goyon bayan al’ummar Kano a zabe mai zuwa.

  • Kyan Alkawari Cikawa
  • Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya

Matasan sun yi kira da a cire Ganduje ne daga kan mukamin shugaban jam’iyyar APC sakamakon gazawar da ya yi wajen samun nasara a zaben Gwamnan Jihar Kano.

Matasan sun yi wannan kira ne a Jihar Kano lokacin wani taron manema labarai karkashin jagorancin Ali Mai Sango, inda ya bayyana cewa dawo da Kwankwaso cikin APC zai kara wa jam’iyyar tagomashi a Jihar Kano da zai iya tabbatar da cewa an samu nasara a 2027.

A cewarsa, Kwankwaso ya san duk wata lago na siyasar Kano da ma Arewacin Nijeriya gaba daya wanda zai iya tabbatar da cewa Tinubu ya samu nasarar sake lashe zaben shugaban kasa a karo na biyu.

Ya yi ikirarin cewa Ganduje ya rasa alkiblar siyasarsa a Jihar Kano, amma idan har Kwankwaso ya dawo APC, zai daga kimar jam’iyyar zuwa wani mataki na gaba a zabe mai zuwa.

Kar Ka Dauki Wannan Shawara – Dattawan APC Na Kano

Sai dai kuma dattawan jam’iyyar APC a Jihar Kano sun siffanta kungiyar da ke kiraye-kirayen cire shugaban na jam’iyyar APC, Abdullahi Umar Ganduje a matsayin haramtaccen kungiya da ‘yan adawa suka kafa a jihar.

Dattawan sun bayyana cewa wannan haramtacciyar kungiya ce wanda aka kafa ta domin farfagandar siyasa mai makon mayar da hankali kan abun da ya dace, amma sun fake da kiraye-kiraye sai an cire shugaban jam’iyyar APC wanda ya shafe shekara 5 yana gwagwarmaya kan samuwar wannan gwamnati.

A cikin sanarwar da kungiyar dattawan APC na Kano suka fitar da ke dauke da sa hannun Abubakar Indabawa da Musaddik Wada Waziri bayan ganawa ta musamman, ta bukaci Shugaba Tinubu da daukacin ‘yan Nijeriya da su yi watsi da kiraye-kiraye duk wasu matasa da suke kiran a sauke Ganduje.

A cewar dattawan, a bayyana yake cewa ‘yan adawa ne suka dauki nauyin wadannan matasa domin raba kawunan mambobin jam’iyyar APC ta hanyar yin kira da a cire shugaban jam’iyyar na kasa.

Sun kara da cewa suna kiran kansu matasan APC amma ba a san su ba a jam’iyyar, kawai an dauki nauyinsu ne domin kawo radani a APC, sai dai kuma ba za su yi nasara ba.

Sun ce, “An dai dauki nauyin wadannan matasa ne domin kawo rudani a APC na yin kiraye-kiraye na sai an cire shugaban jam’iyyar wanda ya samu nasarar sasanta fusatattun ‘ya’yan jam’iyyar a wasu jihohi kamar irinsu Ondo da Ribas tun lokacin da ya amshi jagoranci na tsawon wata 7.”

Dattawan sun ce wadannan matasa suna makiyan Ganduje ne saboda sun ga cewa shi kadai ne daga tsofaffin gwamnonin Arewa da ya bai wa Shugaba Tinubu kuri’u mafi rinjaye a zaben shugaban kasa a 2023.

Idan za a iya tunawa dai an fitar da wani rahoto mai cewa Shugaban kasa Tinubu ya bukaci Ganduje ya shirya da Kwankwaso da dukkan mutanen da suke shirin shiga APC.

An dai ta yada wannan rahoton ne bayan da shugaban kasa ya kammala tattaunawa da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a Jihar Kano bayan da kotun koli ta zartar da hukuncin tabbatar da zaben Abba Kabir Yusuf a matsayin halartaccen gwamnan Jihar Kano.

Shugaban kasan ya yi kira ga dukkan masu ruwa da tsaki na Jihar Kano su kai zuciya nesa tare da tattaunawa da mutanen da suke shirin shiga jam’iyyar APC, domin samun hadin kai da kuma ci gaba jihar.

A yayin da wasu suke ganin cewa rahoton kiran da shugaban kasa ya yi wa Ganduje na sasantawa da Kwankwaso ba shi da tushe ballantana makama.

Yanzu haka dai mutane da dama sun zura na mujiya su ga ko dai Kwankwaso zai dawo APC ko kuma zai ci gaba da zama dan jam’iyyar adawa, lokaci ne kadai zai tabbatar da hakan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
An Cafke Mutumin Da Ya Kitsa Labarin Sace Kansa Don Karɓar Kuɗin Fansa Wurin Ɗan’uwansa

'Yan Bindiga Sanye Da Hijabi Sun Kashe 'Yan Sanda 2 A Katsina

LABARAI MASU NASABA

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version