Kisan Lauya: Gwamnan Legas Ya Gana Da Sufeton 'Yansanda
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kisan Lauya: Gwamnan Legas Ya Gana Da Sufeton ‘Yansanda

bySadiq
3 years ago
Legas

Babban sufeton ‘yansandan Nijeriya, Usman Baba, ya gana da gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, a hedikwatar rundunar da ke Abuja, inda suka tattauna, kan hanyoyin da za a bi domin yi wa lauyar da wani jami’in dan sanda ya kashe a Legas.

LEADERSHIP ta rawaito cewar gwamnan Jihar Legas ya yi alkawarin bai wa ‘yansanda goyon baya wajen ganin an yi adalci a cikin shari’o’in da ke kass kuma hada kai da ‘yan sanda kan shirye-shiryen bayar da shawarwari don ilimantar da ‘yan kasa kan fahimta da mutunta dokokin kasar don kyautata alaka da su.

  • Sin Ta Fadada Samar Da Kwayoyin Ibuprofen Da Paracetamol 
  • An Gurfanar Da Matashi A Kotu Sakamakon Lakadawa Dan Sanda Dukan Kawo Wuka

Ya kuma bayyana cewa, gwamnatinsa za ta hada kai da ‘yansanda domin gudanar da kwasa-kwasai, horaswa da sauran hanyoyin tantance jami’an ‘yansanda a kowane fanni na aikin dan sanda.

Hakazalika Gwamna Sanwo-Olu ya jaddada bukatar samar da wasu kayan aiki kamar na’urorin daukar hoto na jiki, makamai, da dai sauransu, don dakile yawan amfani da iko da inganta aikin ‘yansanda.

A halin da ake ciki, Sufeton’yansandan yayin da yake mika ta’aziyyarsa ga iyalai da kuma ‘yan uwan ​​mamaciyar, ya tabbatar da cewa za a bi diddigin lamarin har sai an yin adalci.

Kakakin ‘yansandan, CSP Olumuyiwa Adejobi, ya ce Sufeton ya kuma bayyana cewa rundunar tana aiki tare da babban mai shari’a na Jihar Legas domin tabbatar da cewa an gurfanar da mai laifin a gaban kotu da ke da hurumin yin shari’a domin zama izina ga wasu.

Sufeto-Janar na ‘yansandan ya kuma bukaci dukkan jami’an da su kiyaye mutunta doka da kuma hakkin kowa, wanda shi ne babban jigon aikin ‘yansanda duk da cewa ya bukaci jama’a da suke bai wa jami’an ‘yansanda hadin kai.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Labarai

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
Next Post
Za Mu Bai Wa Iyalan Wadanda ‘Yan Bindiga Suka Kashe 1m Kowane – Bala Mohammed

Za Mu Bai Wa Iyalan Wadanda 'Yan Bindiga Suka Kashe 1m Kowane - Bala Mohammed

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version