Ko Kananan Sana’o’i Na Biya Wa ‘Yan Nijeriya Bukatunsu?
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ko Kananan Sana’o’i Na Biya Wa ‘Yan Nijeriya Bukatunsu?

byHussaini Najidda Umar
3 years ago
Sana'o'i

Abu na gaba da zan kuma tattaunawa a nan shi ne shin ko wadannan kananan sana’oin da ‘yan Nijeriya suke yi suna biya musu bukatunsu? A nan zan ce eh, suna biya musu sai dai kawai ba kamar yadda ake so ba.

Musamman yanzu da abubuwa suka yi tsada saboda matasalar tashin kayyakin yau da kullum. Wannan kuwa dalilai ne masu yawan gaske da suka jawo wannan tsadar tun da ba wai kawai Nijeriya ba ce take fama da wannan matasalar har da sauran kasashen duniya.

  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Yara 3, Sun Bukaci Kudin Fansa Naira Miliyan 100 A Jihar Kogi
  • Wasu Gwamnatocin Kasashe Sun Nanata Matsayinsu Na Tsaiwa Tsayin Daka Kan Manufar Kasancewar Kasar Sin Daya Tak A Duniya

Wane abu ne mai karamar sana’a ya dace ya yi a irin wannan lokaci na tsadar rayuwa da tsadar kaya? Abin da ya kamata mai karamar sana’a ya yi a wannan lokaci shi ne: Na daya, ya san me yake samu.

Ina nufin shin kasuwancin nasa ya na bashi riba ko a’a, a nan ina so na fada wa mai karatu cewa akwai mutane da suke sana’a kullum amma ba su san me suke samu ba.

Saboda ba sa yin lissafin riba da faduwa. Shi ne ya sa sai ka ga dan kasuwa lokaci guda ya karye ya rasa menene dalili, dalilin kuwa shi ne, shi da kansa ne ya cinye duk ribar da yake samu a kasuwancinsa.

Saboda haka ya zama dole mai sana’a ya rika rubuta abin da yake samu a kullum.

Sannan kuma ya rika sanin kullum idan ya tashi daga kasuwa me ya samu riba ko akasin haka. Duk dan kasuwa ba sai a fada masa yadda ya kamata ya yi lissafin ba domin ya sani.

Saboda haka abu ne mai kyau mai karamar sana’a ya san me yake samu kullum ta hake ne yake da ma’auni a hannunsa yadda kullum zai rika auna kasuwancinsa.

Sannan abu na biyu shi ne dan kasuwa ya san inda kasuwacinsa yake so ya kai shi.

A nan ina nufin duk wani mai yin sana’a ya rubuta a takarda manufofinsa da abin da yake so ya cimma a karshe.

Misali, mutum zai shiga kasuwanci ya ce yana so ya tara miliyan goma a shekara biyu ko uku. A nan dan kasuwa shi ne zai zayyana hanyoyin da zai bi ya tara kudin.

Sannan kuma ya rinka bin duk wannan ka’idojin da manufofin da ya rubuta. Ana so duk dan kasuwa komai kankantar jarinsa ya kasance ya na da manufa da burin inda yake so kasuwancinsa ya kai shi.

Akwai kamfanoni da yawa a kasashen duniya da suka fara da kadan-kadan amma saboda sun yi tsari mai kyau da zayyana inda kasuwancinsu suke so ya je a shekarun da mutum ya tsara za’a ga wannan kamfanin ya kai.

Har ila yau, duk dan kasuwa ya sani cewa makomar kasuwancinsa tana hannunsa, a nan shi ne mai ruwa da tsaki ko mai wuka da nama ta komai na kasuwancinsa.

Shi ne ya sa dole dan kasuwa ya yarda da kasuwancin da yake. Saboda yawancin ‘yan kasuwa suna yin kasuwanci amma ba sa son kasuwacin a ransu, shi ne dalilin da ya sa sai mutum ya ga kasuwancin nasa bai kai shi ko ina ba.

Dole ne mutum ya yarda da abin da yake kada a tambaye ka ka ce ‘to gamu nan dai wannan kasuwancin dai muna yinsa ne kawai’. Kada dan kasuwa ya rinka fadar haka saboda yana nuna bai yarda da kasuwancin ba, shima kuwa kasuwancin ba zai yarda da shi ba.

Abu na ga ba shi ne, duk mai karamar sana’a ya saka a ransa cewa wannan sana’ar ita ce rayuwarsa. A nan ina nufin sana’arka ta zamanto maka ita ce abokiyar rayuwa, yadda idan wani abu ya same ta ya sami rayuwarka.

Ta ya ya za’a mayar da kasuwanci ya koma abokin rayuwa?, hanya daya ce tak.

Ka yarda a ranka cewa idan babu ita babu kai. In dai ka yi haka to hakika kasuwancinka zai kai ka inda kake so musamman idan ka tsara manufofin masu inganci da kuma yiwuwa. Kada ka kirkiri abin da ba zai yiwu ba. Kada ka zauna ka rubuta ka ce kana a kwana dari sana’arka ta tara maka Naira miliyan Dubu, idan ka yi haka to ka fara tambayar kanka nawa ne jarin da ka zuba da zai kawo maka Naira Biliyan dubu?

Wannan shi ne burin da ake cewa ba zai yiwu ba. A koda yaushe ka gina kasuwancinka a kan gaskiya da amana, saboda wadannan abunbuwan guda biyu su ne tushen ci gaban duk wani kasuwanci da mutum ya sa a ransa zai fara. Sannan abu na karshe mai son yayi kasuwanci, kada ka ko ki taba shiga kasuwancin da ba ka ko ki da ilimi a kai.

Wannan shi ne babban kuskuren da mutane suke yi a yanzu na shiga kasuwancin da ba su da ilimi a kansa. Allah Ya kiyaye.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC
Sana'a Sa'a

Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

August 3, 2025
Sana’ar Hada Sabulun Aloe Vera
Sana'a Sa'a

Sana’ar Hada Sabulun Aloe Vera

February 1, 2025
Masu Harkar PoS Sun Bayyana Dalilin Karin Kudin Cire Kudi
Labarai

Masu Harkar PoS Sun Bayyana Dalilin Karin Kudin Cire Kudi

November 22, 2024
Next Post
Amfanin Manhajar XENDER A Wayoyin Hannu

Amfanin Manhajar XENDER A Wayoyin Hannu

LABARAI MASU NASABA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version