Ibrahim Ibrahim">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Korona: Gwamnatin Kaduna Ta Umarci Ba’arin Ma’aikata Su Yi Aiki Daga Gida

by Ibrahim Ibrahim
December 21, 2020
in LABARAI
1 min read
Gwamnatin Kaduna
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Gwamnatin Jihar Kaduna karkashin jagorancin Gwamnan jihar, Malam Nasiru Ahmad El Rufa’i, ta kara daukar kwakkwaran mataki na dakile bazuwar cutar korona, bayan sanar da rufe makarantu da wuraren taron biki da Gidajen rawa.

A wani sako da Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufa’i, ya fitar ya sanar da cewa, daga ranar Litinin 21 ga Disamba, 2020, ma’aikatan Jihar kaduna ‘yan kasa da mataki na 14 su ci gaba da zama a gida da gudanar da ayyukan su daga gida har sai abin da hali ya yi.

samndaads

Jihar Kaduna na daya daga cikin jihohin da aka tabbatar da samun hauhawar alkaluman masu kamuwa da korona a kowacce rana a ‘yan kwanakin nan.

A makon da ya gabata ne Gwamnatin Jihar Kaduna ta fitar da sanarwar cewa ta rufe makarantu kafin daga bisani ta sanar da cewa ta bayar da umarni rufe wuraren taron bikin da Gidajen rawar disko.

A ranar Alhamis ne Gwamnatin Jihar Kaduna ta bayar da umarnin rufe dukkan wasu wuraren taron biki, Gidajen rawar disko, da cibiyoyin motsa jiki, a wani yunkuri na dakile yaduwar kwayar cutar korona a karo na biyu.

Kazalika, Gwamnatin Jihar kaduna ta takaita harkokin wuraren sayar da abinci; babu zama a ci, sai dai a kunshewa mutum abincinsa ya tafi da shi, duka dai domin ragewa cutar karsashi. A cewar Gwamnatin Jihar Kaduna.

SendShareTweetShare
Previous Post

’Yan Bindaga Sun Yi Garkuwa Da Sarkin Ankpa A Jihar Kogi

Next Post

Tsaro: Gwamnatin Katsina Za Ta Hada Kai Da Tsofaffin ’Yan Sanda

RelatedPosts

Man Fetur

Kudirin Dokar Man Fetur Zai Bai Wa Nijeriya Damar Cin Gajiyar Albarkatunsa – Majalisar Dattawa

by Ibrahim Ibrahim
2 hours ago
0

Daga Muhammad Maitela, Shugaban majalisar dattawa, Sanata Ahmad Ibrahim Lawan...

Jobe

Ma’aikata Da ’Yan Fansho Ke Wawashe Rabin Kudin Katsina, Cewar Kwamishina Jobe

by Ibrahim Ibrahim
2 hours ago
0

Daga Sagir Abubukar, Kwamishinan Kasafin Kudi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki...

Rasuwar

Ana Cigaba Da Jimamin Rasuwar Mai Shari’ a Rabiu Danlami A Kano

by Ibrahim Ibrahim
3 hours ago
0

Daga Haruna Akarada, Ana cigaba da gudanar da ta’aziyya ta...

Next Post
Gwamnatin Katsina

Tsaro: Gwamnatin Katsina Za Ta Hada Kai Da Tsofaffin ’Yan Sanda

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version