Khalid Idris Doya">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Korona: Har Yanzu Babu Ranar Bude Makarantu A Jihar Kaduna

by Khalid Idris Doya
January 19, 2021
in LABARAI
2 min read
Ranar Bude Makarantu
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

 Dukkanin makarantun Firamare da na sakandari da suke jihar Kaduna har zuwa yanzu za su cigaba da kasance a kulle duk kuwa da cewa gwamnatin tarayya ta bada damar bude makarantun a sassan kasar nan.

Kwalejin kimiyya da fasaha ta KadPoly da jami’ar karatu daga gida wadanda suka roki a ba su damar su sake bude makarantun domin baiwa dalibai damar zana jarabawa ne kawai aka amince musu sake bude makarantun biyu.

Babban sakataren dindindin na ma’aikatar ilimi ta jihar, Misis Phoebe Sukai Yayi, ta shaida hakan cikin sanarwar da ta fitar a ranar Lahadi.

Ta ce: “Mun sani gwamnatin tarayya ta ce a sake bude makrantu a ranar Litinin 18 ga watan Janairu, biyo bayan sake kulle makarantun da aka yi sakamakon barkewar korona a zango na biyu.

“Duk da gwamnatin tarayya ta ayyana ranar 18 ga Janairu a matsayin ranar bude makarantu, amma jihar Kaduna har yanzu ba ta ayyana ranar budewa ba.”

Ta kara da cewa, har zuwa yanzu gwamnatin tana duba yanayin halin da ake ciki, kana sun bada tabbacin sanar da jama’a da zarar an dauki wani mataki akasin wannan.

“A ranar Litinin 18 ga Janairu ma’aikatar ilimi za ta gana da masu ruwa da tsaki a bangaren ilimi a jihar Kaduna. Sannan, ma’aikatar lafiya za ta mana bayani kan halin da ake ciki dangane da kesa-kesan korona domin baiwa gwamnati shawarorin da suka dace ta dauka nan gaba,” inji ta.

Ta ce, kwalejin KadPoly da jami’ar karatu daga gida ne kawai aka amince musu su bude bisa rokon da suka yi na neman zana jarabawa zalla da aka ba su dama, ta kuma ce sauran manyan makarantun jihar su jira har zuwa lokacin da gwamnati za ta dauki mataki na gaba kan lamarin bude makarantun.

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Za Ta Gina Kwalejin Kimiyya Ta Farko A Borno

Next Post

Abubuwan Al’ajabi A Zaben Kananan Hukumomin Kano

RelatedPosts

An Yi Wa Mukarraban Buhari Rigakafin Cutar Korona

An Yi Wa Mukarraban Buhari Rigakafin Cutar Korona

by Khalid Idris Doya
7 hours ago
0

  Shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Farfesa Ibrahim Gambari, ayau...

Farashin Gangar Danyen Man Fetur Ya Kai Dalla 71.28

Farashin Gangar Danyen Man Fetur Ya Kai Dalla 71.28

by Khalid Idris Doya
8 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim A karon farko a 2021, farashin mai...

Naira

Naira Na Shirin Sake Faduwa Warwas – FMDQ

by Khalid Idris Doya
15 hours ago
0

Za Ta Iya Kai Wa Dala 500 Cikin Mako Mai...

Next Post
A duniyar Nijeriya ta yanzu, da yawan mutane da ma masu lura da al’amuran yau da kullum su na kallon gudanar da zabukan kananan hukumomi

Abubuwan Al’ajabi A Zaben Kananan Hukumomin Kano

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version