Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home MANYAN LABARAI

Korona: Ku Mika Matar Sheikh El-Zakzaky Cibiyar Killacewa

by Muhammad
January 26, 2021
in MANYAN LABARAI
1 min read
Zakzaky
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
  • –Umarnin Kotu Ga Gidan Yarin Kaduna

Daga Rabiu Ali Indabawa,

Babbar Kotun Jihar Kaduna ta umarci mahukuntan gidan yari dake Kaduna da su gaggauta mika Malama Zeenat, matar Sheikh Ibrahim El-Zakzaky, jagoran mabiya dari’ar Shi’a a Nijeriya, zuwa cibiyar killace mutane, domin a duba lafiyarta bayan da bayanai suka nuna cewar ta kamu da cutar Korona.

samndaads

A makon jiya ne Mohammed, dan Sheikh El-Zakzaky, ya sanar da cewa, mahaifiyarsa, Malama Zeenat, ta kamu da cutar ta Korona, amma an hana fita da ita zuwa cibiyar killacewa.

Lauyan Sheikh El-Zakzaky, Femi Falana, ya gabatar da sakamakon gwajinta na takardun asibiti da suka nuna Malama Zeenat din na bukatar kulawa, saboda yanayin lafiyarta.

A hukuncin da ta yanke ranar Litinin, kotun ta bayar da umarnin a gaggauta mayar da Zeenat zuwa cibiyar killacewa mallakar gwamnati, domin ta fara karbar maganin cutar Korona.

Tun a shekarar 2015 gwamnati ta tsare Sheikh El-Zakzaky tare da matarsa biyo bayan wata arangama a tsakanin magoya bayan Shi’a ta IMN da dakarun rundunar soji a garin Zariya da ke Jihar Kaduna.

Femi Falana, lauyan El-Zakzaky kuma Babban Lauyan mai lambar ‘SAN’, ya roki kotun ne don ta yi la’akari da shaidun da ya gabatar wajen bayar da wancan umarni na sakin Zeenat din, domin ta samu kulawa a cibiyar killacewa kamar yadda hukumar NCDC mai yaki da cututtuka ta tsara tun bayan barkewar annobar Korona a duniya.

SendShareTweetShare
Previous Post

Kudirin Dokar Man Fetur Zai Bai Wa Nijeriya Damar Cin Gajiyar Albarkatunsa – Majalisar Dattawa

Next Post

Ya Kamata Kasashen Duniya Su Gudu Tare Don Su Tsira Tare

RelatedPosts

'Yan Adaidaita

An Sasanta Yajin Aikin ’Yan Adaidaita Bayan… Motocin ‘Kano Line’  Sun Koma Jigilar Jakara-Kasuwa

by Muhammad
6 days ago
0

Babu Hanunmu A Ciki Wannan Yaji – Shugaban ’Yan Adaidaita...

Adaidaita

Yajin Aikin Adaidaita: Acaba Ta Dawo A Kano

by Muhammad
7 days ago
0

Ya Jefa Jama’a Cikin Tsaka Mai Wuya Yadda Aka Koma...

Masu Garkuwa

Tattaunawa Da Masu Garkuwa: Yadda Gwamnonin Kaduna Da Neja Suka Raba Gari

by Muhammad
1 week ago
0

Shin Sheikh Gumi Ne Ya Raba Tsakani? Daga Nasir S....

Next Post
Ya Kamata Kasashen Duniya Su Gudu Tare Don Su Tsira Tare

Ya Kamata Kasashen Duniya Su Gudu Tare Don Su Tsira Tare

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version