Kotu Ta Dage Shari'ar Wanda Ake Zargi Da Auran Jikarsa A Zamfara 
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Dage Shari’ar Wanda Ake Zargi Da Auran Jikarsa A Zamfara 

byHussein Yero
3 years ago
Kotu

Wata babbar kotun shari’a Musulunci da ke karamar hukumar Tsafe a jihar Zamfara, ta dage ci gaba da sauraron karar da aka shigar kan wani mutum da ake zargi da auren jikansa.

Alkalin kotun, Malam Bashir Mahe, ya dage ci gaba da sauraren karar domin bai wa lauyan wanda ake kara, Abubakar Ayuba, damar yin nazari kan tuhume-tuhumen da ake yi wa wanda yake karewa.

  • Kotu Ta Yanke Wa Matashi Hukuncin Sharar Titi Da Bulala 12 A Kano
  • Ban Taba Goyon Bayan Tinubu Don Ya Zabe Ni A Matsayin Mataimakinsa Ba – Shettima

Hukumar Hisbah ce ta shigar da karar, inda take neman a warware auren da aka daura shekara 20 da ta gabata.

Hisbah ta shaida wa kotun cewa, auren da aka yi tsakanin Malam Musa Dangote da Wasila Musa ‘yar yayansa, ya saba wa dokokin shari’a da kuma tsarin shari’ar Musulunci.

Hukumar ta ce ta shigar da kara a kan ma’auratan ne bayan kokarin da Majalisar Shawarar Malaman addinin musulunci (Shura) da Masarautar Tsafe suka yi na ganin abun bai je kotu ba abi maslahar abun ya ci tura, inda magidanci ya ce ba za ta sabu bindiga a ruwa ba.

Lauyan hukumar Malam Sani Muhammad, ya shaida wa kotun cewa binciken da hukumomin addinin musulunci daban-daban da masarautar suka yi ya nuna cewa ma’auratan da suka yi aure a 1999 suna da alaka kai tsaye ta jini don haka ya haramta aure a tsakaninsu.

Muhammad ya ce, matakin ya saba wa koyarwar addanin Musulunci kamar yadda ya zo a cikin Alkur’ani sura uku aya ta 23.

Don haka ya roki kotu da ta gaggauta yanke auren.

A halin da ake ciki, Ayuba, ya musanta zarge-zargen kuma ya bukaci samun damar bin rahoton binciken hukumar da ta gabatar a matsayin shaida.

Ayuba ya kuma bukaci a ba shi lokaci domin nazarin tuhumar da kuma shirya kariya.

Alkalin kotun ya bayar da umarnin mika rahoton binciken hukumar ga lauyan da ke kare wadanda ake kara sannan, ya ba shi kwanaki biyar ya yi nazari tare da bayar da amsa gamsasa a gaban kotu.

Daga nan ne alkalin ya dage zaman domin ci gaba da sauraren karar zuwa ranar Litinin mai zuwa.

Wakilinmu ya ruwaito cewa Musa mai shekaru 35 ya haifi ‘ya’ya takwas a cikin auren shekara 20 da suka yi, don yanzu haka ake neman warware shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Akwai Kwanciyar Hankalin Yin Kasuwanci A Nijeriya — Lai Mohammed

Akwai Kwanciyar Hankalin Yin Kasuwanci A Nijeriya — Lai Mohammed

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version