Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Mallakawa Hukumar AMCON Kamfanin Osigwe Foods Saboda Bashi

by
4 years ago
in KASUWANCI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Mai shari’a Saliu Saidu na babban kotun tarayya dake yankin Legas ya zartar da hukuncin cewa Hukumar nan mai tasrifin kaddarori ta kasa AMCON ta karbe gudanar da kanfanin sarrafa abinci ta “Osigwe Foods and Agro Industrial Company Limited” wanda mallakin Cif Anselm Kayode Mohammed ne, bayan da Hukumar AMCON ta shigar da karar neman yin haka.

Hukumar AMCON na bin kanfanin sarrafa abincin Naira Biliyan 5 wanda ita ma ta shiga tsakanin kanfanin ne a kan wasu kudade da suka fito ta Union Bank da Unity Bank da Ecobank da kuma rusashiyar FinBank.

Hukuncin ya kuma hada da gidan shugaban kanfanin dake lamba17, Sowemimo Street, Ikeja GRA, a jihar Legas, wanda bayan shi da iyalisa har da ‘yan haya a cikin gidan, kamar dai yadda sanarwar da aka fitar ranar Litinin ta nuna.

Labarai Masu Nasaba

Kimanin Masarar Naira Biliyan 30 Aka Yi Asara Sakamakon Matsalar Tsaro A 2020 – Manoma

Gwamnati Ta Zargi ‘Yan Nijeriya Mazauna Waje Da Taimaka Wa Nakasa Attalin Arziki

Tuni dai Hukumar AMCON ta nada Cif Robert Ohuoba a natsayin wanda zai kula da harkokin gudanarwar kanfanin na Osigwe Foods and Agro Industrial Company Limited dake Iju Gudugba Billage kan hanyar Agege Iju Waterworks a karamar hukumar Ifako-Ijaiye ta jihar Legas.

ADVERTISEMENT

Sanarwar ta ci gaba da bayanin cewa, “Dokan ya fara aiki ne a dai-dai karfe 2;30 na ranar Talata 19 ga watan Fabrairu 2018, in da za a mallaki gidan Cif Anselm Kayode Mohammed da kuma kanfanin Osigwe Foods and Agro Industrial Company Limited”

“Mai shari’a Saidu, ya anince da nada Cif Robert Ohuoba domin ya zama mai lura da harkokin kasuwanci da kaddarorin kanfanin Osigwe Foods and Agro Industrial Company Limited a duk inda suke matukar suna yankin da kotun nan ke da iko. Matukar kaddarorin na kanfanin “Osigwe Foods and Agro Industrial Company Limited” ko kuma na mai kanfanin Cif Anselm Kayode Mohammed ne.”

Kotun ta umurci Shugaban ‘yansanda na kasa da kwamishinonin ‘yansanda na jihohin tarayyar kasar nan da su taimaka wa ma’aikacin kotun wajen tabbatar da wannan dokan, dai-dai da sashi na 4 na dokokin ‘yansanda da sashi na 287 (3) na kudin tsarin mulkin kasar nan.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Za Mu Fara Daukar Matakin Kare Kanmu –Shugaban Fulani Na Kasa (I)

Next Post

Jihar Delta Za Ta Gina Kananan Rijiyoyin Mai Guda Dubu 30,000

Labarai Masu Nasaba

Manoma

Kimanin Masarar Naira Biliyan 30 Aka Yi Asara Sakamakon Matsalar Tsaro A 2020 – Manoma

by
10 months ago
0

...

Gwamnati

Gwamnati Ta Zargi ‘Yan Nijeriya Mazauna Waje Da Taimaka Wa Nakasa Attalin Arziki

by
10 months ago
0

...

Bankuna

Kasuwanci Na Raguwa Ne A Nijeriya Sakamakon Matsalar Tsaro – CBN

by
10 months ago
0

...

Bankin Duniya

Abubuwa 10 Da Babban Rahoton Bankin Duniya Ya Bayyana Game Da Nijeriya  

by
10 months ago
0

...

Next Post

Jihar Delta Za Ta Gina Kananan Rijiyoyin Mai Guda Dubu 30,000

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: